Header Ads
Showing 285001 words to 287659 words out of 287659 words

Chapter 96 - KURKUKUN ƘADDARA! (TAKUN FARKO) BY By Boss Bature [www.aihausanovels.com.ng].txt

Ads the beginning of article before Image

10 Jul 2024

1813

Ads at the middle of Article

Daga yau ba zaki sake gani na ba, duk wani taimako daya dace inyi maku na riga nayi, yanzu saura ku ya rage ku fara naku, Zamu jira har zuwa lokacin da zaku dawo mana da kyakkyawan sakamako, Sai dai bamu da tabbacin zamu kai lokacin a raye nida mahaifiyata ko kuwa....." bai ƙarasa Maganar ba Angel ta faɗa jikin shi ta rungume shi sosai ta fashe da kuka mai sautin gaske, Hannayen shi biyu ya ɗaura a saman bayanta ya ƙanƙame ta sosai tamkar ƴar cikin shi, Sun ɗauki tsawon lokaci rungume da juna, kafin daga bisani taji kanta ya fara sara mata, nan ta ke idanuwan ta suka lumshe bacci mai nauyi yai awon gaba da ita.........

❤PRISONERS❤

Tsawon lokaci da su Batul su ke ta faman bubbuga ƙofar toilet, Angel tana aciki tana bacci kanta jingine da bango, Salsabeel ne Ya dawo da ita tun da jimawa, tasha uban baccin ta hankalinta akwance yayin da ƴan uwanta su ka shiga matsananciyar damuwa na rashinta.


Ba ta tashi farkawa ba, Sai da dare Ya tsala Lokacin Sun yi nisa acikin baccin su, A hankali ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta, Yayin da la66anta ke ambaton Sunan Allah, Wata irin kasala ta ke ji a jikinta sam babu kuzari, duk yinin yau bata ci abinci ba, Ko ruwa bai gifta maƙoshinta, azababbiyar yunwa ce ta addabe ta, daƙyar ta samu ta yunƙura ta miƙe tsaye Tana ƙarewa toilet ɗin nasu kallo, kamar ranar ta fara ganin shi, Hasken filitar da su ka ajiye acikin shi ce ta gaure ko'ina, Bakomai ne ya faɗo mata acikin ranta ba, Fa ce maganganun da Salsabeel Ya faɗa mata, tamkar a mafarki ta ke tariyo komai da ya faru a tsakanin su, kwokwanto ta soma yi a cikin zuciyarta Anya da gaske ne Haɗuwar su da shi? Gani ta ke yi kamar haduwarta mafarki ce, da sauri ta juya tare da ɗaura kyawawan idanuwanta kan tukunyar fulawar nan da ke ajiye saman floor, Walking slowly ta nufi tukunyar, zuƙunnawa ta yi agabanta idanuwanta akan furen Danish, A tsanake ta ke tariyo duk wani abu da Salsabeel Ya faɗa mata dangane da shi, ba za ta Iya misalta irin ƙaunarshi da ta ke ji ba, Taji takaicin mayar dashi Giant da su ka Yi, zuciyarta ba ƙaramin tafarfasa ta ke yi ba duk in ta tuna cewa yanzu Danish ɗinta Giant ne mai haɗarin gaske, Tayaya zata Iya tunkarar shi? Ba tare da ta samu matsala ba, ' runtse idanuwanta tayi sosai hawaye na cigaba da wanke fuskarta, idanuwanta sun canza launin, ciwon kanta ya tsananta sosai.


"GENIE!" Ras ta ji gabanta Ya faɗi jin muryar Jamimah, A hanzarce ta miƙe tare da sanya tafin hannunta ta share hawayen da ke tsastsafo mata saman kuncin ta, sai da ta fara zuwa gaban Fanfo ta wanke fuskarta sosai, har ta nufi ƙofa zata buɗe sai kuma ta fasa tunawa da Uniform ɗin Jamimah da bata wanke mata ba, kamar yarda tabar su saman Igiyar shanya haka tayi tozali da su, Matsawa tayi gaban Igiyar ta janyo uniform ɗin, kafin ta zame jam lock ɗin da ke a jikin ƙofar, zuciyarta acike fal da tunanin amsar da zata basu idan suka tambayeta Ina taje?


Slowly ta buɗe ƙofar, ba zato ba tsammani ta yi arba da mutun zaune ya jingina bayanshi jigin bangon sashen toilet ɗinsu, gabanta ba ƙaramin faɗuwa ya yi ba, ta ɗan tsorota kafin ta gane wacece, Ashe batul ce bacci ya ɗauke ta a wurin ita da Jamimah sunƙanƙame juna, yadda kasan ƴan gudun hijran da suka rasa wurin kwana, jamimah sai sambatu take yi tana ambaton sunan Genie, da alama bacci ne ya ɗauke su zaune awurin su kaɗai, ta kwanta da tunanin Angel shiyasa ta ke yin sambatun kiran sunanta, murmushi ta saki yayin da take ƙare masu kallo, Har zuwa ta yi gabansu ta zuƙunna tana ƙare masu kallo kamar zata lashe su saboda tsabar ƙaunar da ta ke yi masu, tunawa da Maganar Salsabeel Yasa tayi saurin miƙewa ba tare da ta tayar dasu daga baccin ba, ta nufi cikin ɗakin su, shigarta keda wuya Tayi arba da Su Deeja kwakkwance saman gadajen su, tsit ɗakin sautin minsharinsu Parveen ya cika ko'ina, mamaki ne ƙarara akan fuskarta, wai ashe dare ya yi bata sani ba? a iya sanin ta tsawon mintuna talatin su ka ɗauka suna yin magana da salsabeel, Kenan Baccin ne mai nauyi ya ɗauke ta A jikin shi? Kuma shine ya dawa da ita? Lamarin ya ɗaure mata kai sosai.

Allah ka ɗai yasan irin farin Cikin da ta ke aciki, Sai ta dinga ganin kamar suna a kwance ne saman Gadan daddynta dake a gidansu, Wani irin annuri ne ya bayyana akan fuskarta, kamar wadda aka yiwa albishir Da gidan Aljanna, Ji ta ke yi kamar ta Zuba ruwa ƙasa ta sha, A ƙalla ta ambaci Alhamdulillah ala Kulli Haal Yafi sau aƙirga, Ta gode ma Allah da wannan ranar domin tasan cewa shine silar komai, Allah maji roƙon bayinsa ne ya kar6i koken su Zai kawo masu ƙarshen Zaman Su A GIDAN KURKUKUN ƘADDARA, Fatan ta Allah yasa Kada su ƙara rasa wani acikin su, tafi so dukansu su tsira atare kamar yarda su ka sha wahala atare, Zuƙunnawa tayi saman gwiwowinta tare da fuskantar gabas ta yi sujud shukr domin nuna godiyarta ga Allah, kafin ta ɗago kanta tuni hawaye sun wanke fuskarta, yau tasha kuka idanuwanta har kumbura sun ɗan yi, bayan ta kammala ta miƙe tsaye

Har zata nufi ɗakin tsohuwa tamira, ta wutsiyar idonta ta hango Haris kwance saman gadonshi, Da sauri ta Kai idonta gare shi, Abun mamaki sai taga Hada Naufal da javed Ga mubeen kwance saman gadonshi, Ga kuma Gabriel kwance ana shi gadon, Azeeza tana agefenshi, Nan bacci ya ɗauke ta, Waro Ido waje tayi bakinta a sake ta ke kallon su, farin Cikinta ya ƙara ninkuwa ɗaya bayan ɗaya ta ke binsu da kallo Agaban gadon haris ta tsaya tana kallon shi, Gwanin ban tausayi, Ya canza mata sosai, Zuƙunnawa tayi gaban gadon shi tsawon mintuna biyar tana bin shi da kallo kafin ta yunƙura ta miƙe ta nufi gadon Javed, bayan ta gama bin su da kallo ta tabbatar da jikinsu da sauƙi, sai taji sanyi aranta.

Ataƙaice daren ranar Angel Ta kashe hasken ɗakin su, Ta koma sashen makewayin su, ta ɗauko Fitila ɗaya, ta kashe haskenta, Cikin duhu ta dinga tafiya tana laluban Hanyar da zata kai ta ɗakin tsohuwa Tamira, cikin sa'a ta samu nasarar shafa jikin bangon da ƙopar ta ke a manne, nan ta ke ta buɗe.

Ajiyar zuciya ta sauke, ba tare da jin shakkar komai ba ta faɗa ciki, bakin ta ɗauke da bismillah, bayan ta shige taja ƙopar ta rufeta, kafin ta kunna Fitilar hannunta haskenta ya gauraye ɗakin sosai tamkar da rana, Mamaki ne ƙarara akan fuskarta, Ganin Gadon ƙarfe da wooden Book shelves Jikin bango, Jerin littattafaine tsoffi da suka daɗe a ajiye cikin shelves ɗin, daga can tsakiyar ɗakin kujeru ne guda biyu, A tsakankanin su madaidaicin teburi ne mai ɗauke da Tea pot da ƴan kofina.

A bun da ya ɗaure mata kai, Kwanakin baya da ta ta6a zuwa ɗakin Ba ta ga gadon ƙarfe da book shelves ɗin ba, sai dai Shufke shufken fulawowi da teburin nan mai ɗauke da teapot, Lallai tsohuwa Tamira ta ƙware wurin Iya Canza ma ɗaki suffar shi Ta hanyar yin amfani da sihirin ta.

Shiga ciki ta yi adai dai gaban teburin ta ɗaura fitilar hannunta, Ba tare da 6ata lokaci ba, ta bazama neman ruwan zam zam, Ko'ina ta shiga dubawa Har ƙarƙashin gado, ba ƙaramar wahala ta sha ba wurin neman shi, ta haɗa uban gumi a kan fuskarta, A ƙarshe ta gano ta a saƙon littattafan da ke a cikin shelf ɗin, (plastic vial) Ƴar Karamar roba kalar wadda ake zuba ruwan allura, wasu kuma suna amfani da ita wurin zuba ruwan turare, farace ƙal duk tsawon shekarun da ta ɗauke ajiye bata canza ba, kana iya hangen ruwan dake acikinta, bai wuci ka yi ma shi kur6a ɗaya ba Ya ƙare, A cikin aljihun wandonta ta zura robar, dama anan ta 6oye takardar adireshin da ya bata na gidan su.

Kafin ta baro Cikin ɗakin sai da ta kashe filitar, Tukunna ta ruƙo handle ɗinta, Cikin duhu ta fito ta nufi toilet dinsu Ta shiga ta ajiye fitilar, bayan ta fito ne, ta samu wuri daga gefen batul ta zauna tare da kai hannu ta janyo jamimah zuwa saman laps ɗinta sosai ta rungumeta a ƙirjinta, A saman kafaɗar batul ta ɗaura kanta, tamkar an wanke mata zuciyarta da ruwan farin ciki, Ba ta runtsa adaren ranar ba, saboda a ƙagare ta ke da gari yawaye, duk don ta samu damar cigaba da gudanar da aikin ta, gaba ɗaya daren idonta biyu ta yi shi, tunanin Danish da ƙofar nan sun tsaya mata aranta, sune abun harinta.

A washe garin ranar da su ka farka daga bacci, ba ƙaramin farin ciki su ka yi ba ganin Angel ɗinsu ta dawo acikinsu, ɗaya bayan ɗaya suka dinga rungumarta a ƙirjin su, haɗi da tambayarta meyasa taƙi buɗe masu ƙopar toilet? Meya faru da ita? Tsawon lokacin da ta shige cikin toilet.

Angel ta ce masu Bacci ne mai nauyi ya ɗauketa, gaba ɗaya sun yarda da maganarta, basu kawo komai aran su ba, Su Haris ba ƙaramin farin ciki su ka yi ba, ganin Angel musamman Gabriel don ba ƙaramin kewarta ya yi ba, jikin nasu babu wadatacciyar lafiya amma da ya ke mazane suna da ƙarfin hali da juriyar 6oye damuwar su, duk don kada su tayarwa ƴan uwansu da hankali, Ita kanta Angel ta lura da yanayin da suke aciki tabbas anyi masu wani mummunan abun da basu son sanar dasu, abunda yasa Angel bata matsa ma su akan su faɗa mata ba, saboda hankalinta ba a kwance ya ke ba, ta ƙwallafa rai akan son aiwatar da alƙawarin da ta ɗaukar wa Salsabeel, in har bata ci nasarar dawo da Danish a cikin su ba, ta kuma gano ƙofar nan to bazata ta6a samun natsuwa ba, ko su Deeja bata sanar dasu ainihin abunda ya faru da ita ba, ta yi hakanne saboda gudun kada murnar da za su yi ta yi silar janyo hankalin giants zuwa gare su, shiyasa ta ɗan jinkirta tana jiran su zo kawo masu abinci, saboda ta ɗauki ruwan zafin da za'a kawo masu, bayan giant ɗin sun tafi, zata ja su zuwa cikin sashen toilet ɗin saita sanar dasu komai, haka ta tsara acikin zuciyarta.

Kamar Giants sun san da shirinta ranar suka ƙi kawo masu Ganye da wuri, Ranta yai mugun 6aci, har sai da ta fara hasashen ko asirin su ya tonu ne shiyasa suka ƙi zuwa kawo masu ganyen, Wuraren marece sai gasu sun shigo ɗauke da farantan ganye da robobin ruwa mai zafin haske, Lamarin ya ɗaure wa su Haris kai ganin An kawo masu ganye amatsayin abincin su, Har tambayarsu Hanna su ka yi meyasa aka canza masu abinci? Nan suka kwashe duk abunda ya faru tsakanin Angel da tsohuwa zafreen suka sanar dasu, Ransu ya 6aci sosai, tsabar tausayin su da su ka ji har ƙwalla sai da su ka zubda masu.

Ko da Giant suka kawo masu ganyen bata bari su hanna sunci ba, duk don saboda Giant su yi saurin tafiya yasa ta kwashe masu ganyen da ke acikin wooden trays ɗin ta zuba su cikin kwandon batul, gaba ɗaya robobin ruwan zafin Angel ta tattarasu duka ta ajiyesu, Ganin sun gama kwashe Ganyen yasa Giants ɗaukar Farantan tare da fucewa daga Cikin ɗakin, kunnuwanta na jiyo mata ƙarar rufe ƙofa ta yi zumbur ta miƙe tare da ɗaukar robobin ruwan guda uku ta nufi sashen toilet ɗinsu Mamaki ya kama su batul ganin ta shiga da robobin ruwa cikin toilet, Hakan yasa suka bi bayanta da sauri don ganin me za ta yi da su.

Bayan sun shisshiga Ciki, tace da Azeeza ta kira su Haris su shigo gaba ɗayan su, da gudu Azeeza taje ta kirasu, bayan sun shigo daga Ciki, taja ƙopa ta datse ta da jamlock.

Atare suka haɗa baki wurin tambayarta"ANGEL WHY KIKA SHIGO TOILET DA BOTTLE WATERS A HANNUNKI? MEYASA KIKA SA AKA KIRA MU GABA ƊAYAN MU".


"BANA SO KUNA YIN MAGANA! KU YI SHIRU KU ZUBA IDO KU GA ABUNDA NAKE SON NUNA MAKU, AMMA KAFIN NAN INASO IN GARGAƊE KU, KOME IDANUWAN KU ZASU GANE MA KU KADA KU KUSKURA KU CE ZAKU YI MAGANA, " Amsa mata su ka yi da toh, zuƙunnawa tayi agaban tukunyar fulawan tare da ajiye robibin ruwan dake a hannunta ƙasa.

"Batul ke da Deeja ku kawar min da tukunyar nan" Da sauri suka sanya hannayensu tare da ɗaga tukunyar suka sauke ta gefe ɗaya.

Buɗe murfin robobin ruwan tayi har tiriri ya ke yi saboda zafin shi, ɗaya bayan ɗaya ta soma ɗaukarsu tana kwarara ruwan jikin bangon da tukunyar ta ke a jingine dashi, wurin yayi shaida saboda da daɗewar tukunyar.

Kowanan su Ya ƙura ido yana kallon ikon Allah, Shin me Angel ta ke son nuna masu ne? Ras gabansu ya faɗi, A matuƙar ruɗe su ka zazzare eyes ɗinsu akan bangon dake tsastsagewa Nan ta ke ginin dutsen da aka yi shafe dashi ya soma 6a66akowa, tamakar an sanya wuƙa an tsargashi haka ya dinga zazzagewa, gaba ɗaya ya rubzo ƙasa, Kallon kallo suka shiga yi atsakaninsu Tsantsar al'ajabi ne ya kamasu, lokacin da tsohon murfin ƙofar ya bayyana a suffar shi, Jikin ƙarfen duk yayi tsatsa.

"Angel menene wannan"? A matuƙar ruɗe suke tambayarta, Ɗagowa tayi tare da kallonsu wani ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta mai nuni da tsantsar farin Cikin da ta ke a ciki, dimples ɗinta duka biyu sun lotsa sosai, Tunkafin ta motsa la66anta da niyar amsa masu tambayarsu, muryar batul ta katse mata hanzarin ta

"Kamar Ƙofar da mu ke nema"? jinjina masu kai tayi alamar eh ta ƙara da cewa"FINALLY MUN YI NASARAR GANO ƘOFAR DA ZA MU BI MU GUDU DAGA CIKIN KURKUKUN ƘADDARA SAI DAI KASH! BOSS TA ƊAUKE ALƘALAMINTA DOLE MU JIRA TAKUN TSAKIYA DOMIN JIN YADDA ZA TA YI DA RAYUWARMU IN ALLAH YA KAIMU DA RAI DA LAFIYA!"

ALHAMDULILLAH END OF TAKUN FARKO🥳🥳🥳🥳🥳

*Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za'ayi adding naka a paid group kuma za'a sanyaka a comment section, Sa'annan Ba'a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*


********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 08138873799


Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************



Ads At the End of Article
Sidebar Ads

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads