Showing 45001 words to 48000 words out of 274096 words
Chapter 16 - DAULA BIYU Complet Document .txt
muke daure nonuwar mu dashi, dashi na daure nawa, amma sauran basu daure nasu ba. Sun barshi yadda suna rawan yana zillo.
Tunda muka gama suka shirya mu, tare da nufar shashin. Muna shiga aka fara mana kid'a, lumshe idanuna nayi tare da jin sautin kidar har cikin kai na. A hankali muka fara rawan, ana watsa mana wani irin ruwa, kafin kace me duk mun bugu, zan iya cewa ban san kome ba, amma tabbas naga lokacin da wanda muka yi fada dashi ya dauke ni, sama sama nake jin kamar ihu da hayaniyar muryan mutane.
Tun daga nan ban kuma fahimtar kome ba, sai da safe. Na tsince kai na a wannan karamin dakin nan dai. Gyara kwanciya nayi zan cigaba da barci naji an sheka min ruwa, zubur na miki tare da kallon mutumin.
"Banza kawai! Insha Allah akan wancan dan luwadin zan rama."
A fusace ya shigo dakin tare da shake min wuya, dariya ya bani nace mishi.
"Toh ba dan luwadi bane? Me yasa ya ajiye kartin maza irinku yana zaka takashin ku..."
Marina yayi tare da ture ni, sannan ya fita. Tashi nayi na shiga ban daki nayi wanka da alwala, nafito tare da sallar ta sallolin da suke kai na, ina cikin addu'o'in ya kuma kawo min abincin.
"Da fatan baka saka min guba ba?"
"Da zaki ci ki mutu ai da ba haka ba"
"Sai dai kai ka mutu domin duk abinda aka min sai na rama akan wancan mara mutuncin."
Na shiga cikin abincina,.haka ya fita yana tsaki a ranshi.
Yana gama shiryawa ya kalle su, sannan yasa kai ya fita.. abubuwan da suke faruwa yake dawo Mishi kan shi, tun daga haduwar shi da yarinyar har zuwa yanzun, takaddarirancin ta yayi yawa dole ya sauke mata shi, dole ya koya mata hankali. Dan haka ya tanadar mata da nau'o'in azaba.
..... Koda naji gidan babu hayaniya,shiryawa nayi tare da barin cikin gidan, na nufi haramtacciyar Fada. Kimanin sati biyu zuwa uku kenan bamu samu damar haduwa da juna ba.
Ina shiga na karasa gurin Maman Jasrah. Zube gwiwata nayi cikin ladabi da biyayya.
"Aikinki yana kyau? Amma yaushe kika koyi fada haka?"
Sosa kai na nayi sannan nace mata.
"Kasancewar munyi fama da hare hare da yaki yasa muka koya dan kare kanmu."
"Kinyi aikin da ya dace saura mataki na gaba, dan banyi tsammanin lokaci guda Mehran zai barki a cikin fadar shi ba, dan haka ki nutsu kema ki koyi halin masarautan ki koyi dabi'ar su."
Daga nan ta shiga daura min darasin mu na gaba. Tare da yadda zan kuma samun shiga cikin gidan sosai.
Wannan littafin na kuɗi ne.
*Allah ka jikan Iyayena 😭😭*
#Mai_Dambu.
[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜
Book 1
Mai_Dambu
BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM
Page 23
Ina cikin sauraronta, sai ga dakaru. Suka shigo cikin gidan. Basu yi wata wata ba, suka saka Ni a gaba. Ban yi musu ba, tunda muka nufi cikin gidan na fahimci ran Mutumin nan ya ɓaci.
Ban d'aga hankalina ba, sai da naga ya saka manyan kartin maza, dai dai fitowar Sultan Mehran, suka shiga zane ni. Tare da tambayana da Izinin waye na fita. Idan na basu amsa tabbas ina tsoron su, idan nayi shiru kuma zasu ji bakin ciki.
Dan haka nayi banza dasu, ganin haka suka ci-gaba da zabgata, sai da suka ga kayan jikina yana yagewa, kai na kwance sabida zunzurutun dukar, wanda ya haifar da zubar jini daga bulalan. Yana zaune ya daura daya akan daya.
Ba kome yake bashi mamaki ba, yadda taurin kai ya hanani ihu, jana suka yi zuwa dakin da nake, lokacin sallah azhar yayi da haka nayi ta bin bango na shiga ban daki, nayi alwala na fito. Sai da na fara sallah ne kuka ya zo min, tare da shashekar.
Kumshe idanun shi yayi tare da kallon Abincin da yake gaban shi ya fara ci a hankali, yana iya jiyo kukanta amma bai da wani damuwa akan haka, sai ma takaici da haushin da take bashi. Ya gaji da sauraron ihunta. Ture abincin yayi tare da ɗaukar bulalan ya nufi d'akin.
"Afwa Sultan Mehran! Ta tuba ba zata kuma ba."
Inji Darakshan, banza yayi da su ya shige d'akin, ganinta yayi ta kai sujada, tana kuka tare da kirariwa Ubangiji, abun ba wai tana yi a fili bane a Zuciyarta ne har ya fito fili.
Kalmar da ya tsaya mishi a rai ya cigaba da hautsina mishi lissafi,
"Ya waduddu Ya Zul-arshin majid! Ya fa'alil limayuri"
Ji yayi kan shi kamar zata fashe abinda yayi niyya ya tsinci kanshi ya kasa aiwatar wa, da sauri ya fito, domin ji yaƙe d'akin tana mishi zafi kamar an hura mishi wuta.
Abinda zuciyar shi ta fara gaya mishi ba kome bane face.
*Lallai yarinyar nan matsafiya ce, kuma zata iya halaka mutanen birnin ka, kayi gaggawan sawa a halakata*
Cikin wani irin tsawa yaji wani shashin zuciyar shi tana cewa.
*Ba matsafiya bace, kayi bincike kafin ka zarta da hukunci*
Take zuciyar shi ta kasu bangare biyu, zama yayi cikin damuwa yana kallon su.
Ganin yadda ya fito yana haki, a fusace suka nufi d'akin, suka tadda ita tana sallah. Cikin fushi Darakshan ya nufeta, kamar wanda aka tura shi dakin wuta, ne zunzurutun zafi dole suka fito basu shirya ba.
Kallon juna suke dashi, bakin shi nason yin magana, amma kamar wanda aka rufe mishi bakin,dan dole yayi shiru yana kallon su. Amma zunzurutun mugunta dariya yake musu a ranshi, musamman yadda suke hada gumi.
Tashi yayi ya wuce sama, daga nan ya hana kowa shigo mishi, ko masu kula dakin shi baya kaunar su shigo mishi.
Gashi dakin shi yayi wani irin datti, abinci ma tsakanin shi da Allah ya kaurace musu, Fudail ne ya fahimci abinda yake nufi, dan haka da kan shi ya saka ni a gaba muka haura har dakin shi, na gyara kome na goge kome, tare da tattara kayan dattin shi ne fito dashi.
Me wanke mishi kayan shi ya amsa, sannan Fudail yace min.
"Akwai dakin girki kece zaki cigaba da mishi girka."
"Akan me?"
"Sabida haka yake bukata."
Kamar zanyi magana sai kuma na fasa, tun daga ranar na koma Jakar Sultan Mehran, kamar zanyi kuka wani lokaci a dakin girkin nake kwana, sakamakon yadda kome dare zai Turo na daga mishi shayi, idan ina barci haka Fudail zai tashe ni.
Kuma dan rashin mutunci, idan na gama abincin sai an sani na ci kafin yaci, ina tsaye zai gama mulkin shi kafin yaci, yana ci yana wulakanta ni, ta Hanyar watsa min ruwa, ko furza min abincin a fuskana, ko kuma ya kwala min kofi, iya wahala ina fuskanta da Mehran. Amma ban tab'a jin ko ganin wata rana zan sami yanci ba.
Yau ma ina kwance, naji ana zungurina, bude ido nayi na kalle shi. Daga shi sai yar kwarjalle, da wata rigar shan iska, da sauri na mike, dan ban tab'a ganin shi ba, ido da ido babu alkyaba. Yau ma dai gashi ne yayi mishi rumfar da fuskar shi. Tsayawa nayi ina kallon fadaddar kirjin shi, me yalwacce da gashin a kwance luf.
Yana rike da kofi a hannun shi, sai juya kofin yake. Banyi aune ba sai ji nayi an saka min kafa, na zube kasa.
Wallahi idan ka gan shi ba zaka tab'a kawowa zai yi irin wannan muguntar ba, amma ina mugu, kamar bashi ba.
Tashi nayi na shiga ƙoƙarin hura wutar, sai na kunna zai kashe, ajiye abin hura wutar nayi a fusace zan fita, make ni mutumin nan yayi, kai na ya bugu da bango. Anan na sume mishi.
Bai damu ba, ya tsallaka ni. Ya fice Daga dakin girkin, dake ranshi yana kaunar shayin kafin ya kwanta, dole ya d'ago Fudail yazo ya watsa min ruwa, tare da taimaka min na hada mishi ruwan zafin, kai na kamar zai fashe, ina aikin ina kuka.
Ina gamawa Na mika mishi zan fita sai gashi ya kuma shigowa, bai magana ba shi lallai sai dai nayi mishi girki, kallon shi nayi dan dare ya raba sosai, haka na shiga aiki babu ji babu gani, kuma yana tsaye. Dakyar na kammala aikin, ina gamawa ya kalle ni, na zauna jagwab. Saka hannun shi yayi tare da zuba abincin gabaki daya.
A razane muka kalle shi, kwalla ce ta shiga cika min ido.
"Yadda ka tozarta Abinci sai Allah ya tozarta ka."
Buge min baƙi Fudail yayi tare da kwashe abincin. Ya mika min.
"sake wani"
"Ba zan girka ba!"
Kallon Fudail yayi sannan ya kalli hanyar fita, yana isowa inda nake ya daki kafana da kafarshi, yadda kuka san an karya itacce haka ya b'alla min kafa sannan ya ficce abin shi. Ihun da nake yasanya Fudail da Darakshan suka kuma shigowa..ganin ina gurnani. Tare da rike kafar da ta lankwashe.
"Kai Amma Sultan Mehran bai." Gyaran murya muka ji, daga bakin kofar koran su yayi daga kitchen ɗin, haka ya juya ya fita shima.
Washi gari kafar ta kumbura sumtum, kuma dan bakin mugunta wai nayi abin karyawa, dole Fudail ya gaya mishi gaskiya.
"Sultan Mehran, yarinyar nan.ba zata iya aiki ba, sabida zazzaɓi da karaya."
Lallai shi zasu renawa hankali dan haka ya juya ban shi.
"A fidda ita."
Haka Fudail yazo ya fita dani, zuwa gidan Me magani Lingesa, suka daura min kafar, bayan nasha bakar azaba.
Duk da ban wuce kwana ashirin a cikin shashin Sultan Mehran ba, amma kuma na sha azaba a cikin gidan. Dan haka na dauki wannan fitar nawa a matsayin abinda Allah ya bani.
---
Ba a san munafukin da ya gayawa Sultanah Hoyam cewa Ai akwai mace a shsshin Sultan ba, sai gashi hankalinta yayi mugun tashi. Yana fada ta tura mishi sakon idan zai koma gida yazo tana son ganin shi.
Kallon dan aikan yayi bai ce mishi kalla ba, sai bayan an tashi ya nufi gidan.
Tunda ya zauna take magana, gashi ta zuba mishi abinci, loma daya ya kai bakin shi, furzawa yayi tare da kallon ta, a hankali ya mike zai fita tace mishi.
"Mehran! Don Allah karka yarda da yarinyar domin kashe ka zata yi! Haka suk.."
"Kenan kece kika kashe Abba na?"
A zabure ta kalle shi jikinta yana rawa, murmushi yayi sannan ya fita daga d'akin, tana ganin ya fita ta kira Narmin, tasaka aka dauko ni, bayan ta min duka da bulala sannan tasaka aka mai dani gurin jinyar da nake tare da cewa za a kai ni. Shashin Amir Hood, a can zan zauna na cigaba da aiki.
~~
Noman.
Sun isa Abu Dhabi, inda suka shiga nima na, babu ni babu labarina, karshe wani ne yace musu.
"Wai kun anan zaku same ta? Tabbas naga me kama da ita a Andulus, dan haka ku tafi can zaku sami labarinta."
Sabon tashin hankali, haka suka sake juyawa suka koma masaukin su, washi gari suka kuma ɗaukar hanya, ta jirgin ruwa.
~~
Wata na daya ina jinya, sannan aka tura ni shsshin Amir Hood, inda yake dauke da matasa maza kusan guda biyu.
Yan biyu ne yaran Abdul Malik, Zuhair da Zunoon.
Yaran matasane da suka haɗu iya haduwa, sai dai basu Mehran ba, Zunoon bai da matsala asalima bai da ra'ayin mata, domin a gefe guda yana da ilimin addini sosai, sakamakon dan uwan shi Zuhair da ya kasance kullum sai na ganshi da yan mata bayi sama da biyu.
Bana sake mishi fuska, kullum na shiga shshsin sa, zan gyara mishi gado, da suka lalata zanyi duk abinda ya dace, idan zan fita ne yake tsare min hanya.
Dauke kai na, nake yi abuna sannan na fita daga dakin, haka ko a Kitchen zai shigo min, sai dai naji duka a mazaunaina, wannan rashin darajar yana min ciwo.
Dan haka na shiga tara shi, ranar da ya cikani zai sha mamaki.
..... Wasa wasa Mehran ya fara kin abincin da ake girka mishi, a hankali ya buɗe musu ido, lallai sai dai su dawo mishi dani, tsuru tsuru suka yi an rasa wanda zai gaya mishi ai Sultanah tasa an mai dani can Shashin Amir Hood.
"Ina yarinyar take?"
Ya tambaye su a tsawace, had'iye yawun suka yi, tare da cewa.
"Sultanah Hoyam ta."
Lumshe idanun shi yayi cikin wani irin b'acin rai, sannan ya bude akan su, yace.
"Waye a cikin ku ya gaya mata akwai mace anan?"
Tsoro da tashin hankali ya hana su magana.
"Afwa Sultan!"
Wani irin cira yake, dan haka ya mazge kamar bai damu ba, amma kasan ranshi yana jagule, sakamakon yadda bakin shi ya sakalkace da diban albarkan hannunta, sannan dan tsaya an sami munafukin da ya saka a ka raba shi da ita, duk sai ya zabga musu rashin mutunci. Yake ayanawa a ran shi.
Share batun yayi dan karsu darsa wani abu a ransu, dan ya fara jin ƙishin ƙishin wai ya damu da bakar fatan da take kula da shi.
A hankali kwanaki suka shiga tafiya sama da baya ma, tun yana iya dauke kanshi baya magana, har takai ya kasa hakuri. Gurin Sultanah Hoyam ya nufa, yadda ya zauna Fahimci abinda yake damun shi.
"Mehran!"
"Me yasa?"
Ta tambaye ta,
"Meke faruwa,?"
"Yarinyar da kika dauka!"
"Wacce?"
Girgiza kai yayi tare da mik'ewa ya nufi hanyar waje, bai kuma mata magana.
Tunda ya bar gurinta bai kuma magana akan Ikram ba, asalima tattara ta yayi ya saka a gefe, sabida rashin hankalin da iyakokin shi da kasar jordan suka sami wata b'araka, haka yasa aka fara shirin tattaunawa, karshe aka sami labarin suna shirin yaki.
Dan haka ya shirya da shida zaratan jarumai su kimamin dari cif. Tafiyar bai da ra'ayin shi amma idan ya tuna matsalar da yake tukarar kasar shi, dan haka ya nufi yakin, dake an san Dakarun SAMAIND basa fitowa kad'an, dan haka suma suka shirya musu.
Tafiyar kwana uku, suka yi tare da tura dan leken asirin su, ya duba musu yawan dakarun, anan suka sami labarin dakarun miliyan uku ne, murmushi Yayi sannan, ya fara musu zanen yadda zasu ci garin da yaki ba tare da sun tab'a talakawan kasar ba. Aikuwa haka ce ya faru, domin shigan dare suka musu, ana tsaka da shagali, suka farmake su. Inda suka kama Sarkin Jordan. Sultan Suhaib Salem.
Tare da duk masu hannun akan a farmake su.
"Ba ra'ayina zubda jinin kowa ba, amma ku da kuka ci amana ta, zaku fuskanci horo."
Daga haka yasa aka sare kawunan su, aka kafa a tsakiyar birnin, bayan ya nimo mutanen da suka dace da masarautan, ya nad'a su a sarakunan kasar jordan.
Sai dai wannan abun ya faru akan Idanun Yar Sarkin Sultan Suhaib Salem, wato Almirah Jennah. Wacce take kuka kamar ranta zai fita, bayan tafiyar Sultan Mehran itama ta....
*Allah ya jikan Iyayena 😭*
Littafin nan na kuɗi ne.
#Mai_Dambu.
[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜
Book 1
Mai_Dambu
BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM
24
Tafiyar kwana bakwai kacal ya kai su Jordan ya kuma dawo dasu, koda aka ce an hango rakuman su. Wani irin murna mutanen gari suke, babu abinda ya kuma burge su kamar yadda ya shigo garin a basaja, aka kasa ta tantance shi a cikin jama'ar shi.
Ya shige cikin Masarautan babu wanda ya gane shi. Tunda ya shigo Masarautan bai tsaya ko ina ba sai shshain Mahaifiyarshi, cikin murna da dauki ta rungume shi.
"Albarka ya baibayi rayuwarka!"
Sake ta yayi sannan ya nufi castle din shi.
Tunda ya shiga ya sami gidan ko ina kal kai, amma babu wannan karsashin da ya d'andana na kwanaki ƙalilan kafin rabuwar shi da Yarinyar. Cogewa yayi daga bakin kofar, cikin takaici ya juya bai ce musu kome ba.
Duk inda ya wuce binshi ake, dan ko takalmi babu a kafar shi. Ya gaji, wata biyu ana niman na uku rabon shi da ita, shi ko dan cikin shi yana niman ta, yana bukatar ta a matsayin baiwar shi da zata mishi abinci. Wannan abun da take karantawa ko take renawa yake son saurarra, yana son ganinta cikin kadaita lokaci tana goho da dungure iya haka ma ya wadatar dashi.
Kai tsaye Shashin Amir Hood ya nufa.
--- Tunda aka kawo ni, Zuhair yake bina da mugun nufi, sau biyu ina kwatar kaina da wuka, domin ya sha giya zai zo yayi ta niman lalata min rayuwa. Yanzun ma na idar da abincin sune na kai inda ake ajiyewa, na shiga wanka, shine ganin ina ban daki ya biyo Ni.
Allah ya taimake ni na saka yar shimi na Kenan, ina saka rigar