Showing 99001 words to 102000 words out of 274096 words
Chapter 34 - DAULA BIYU Complet Document .txt
nayi na kalli mutumin sannan nace mishi.
"Ba a min dole aiki tunda nice nace zanyi toh a zuba min ido."
Kallona yayi sannan ya share tare da nufar hanyar shi na daban, nima nufi gidan nayi. Ina shiga na hango Izmah a kwance a tsakar dakin babu kaya, kowa yana harkan gaban shi. Da sauri na isa gaban ta, tare da cire mayafina na rufe ta dashi, sannan na kalle ta tana kuka. Irin wanda aka tozarta.
Taune bakina nayi ina kallon matan da suke tsaye tare da rike bulala sannan daya daga cikin su tana faɗin.
"Eh munga Wada ce kuma tana da kayan mamaki shine muka duba ko tana da budurcin ta har yanzu." Fashewa tayi da kuka tare da rungume ni.
"Ki mai dani Gulsana, na hadaki da Ubangijin ki!"
Matse kanta nayi a kirjina, ina tuna alkawarin da na dauka a raina.
_Ya Allah kamar yadda ka Hadani ƙaddara da wannan Baiwarka Ya Allah ka bani ikon kare lafiyarta daga duk wani abin cutarwa daga nesa ko kusa_
"Ban san me yasa mutanen duniya suke da zalinci a ransu ba, hmm" nayi wani irin murmushi. Sannan na dauke ta tare da ajiyeta a saman gadon mu, duk da tana da zuri amma dake zuciyata tana zafi bana jin kome a raina.
Rufeta nayi sannan na koma na rufe kofar d'akin, tare da kashe wutar dakin da gayya, ban tab'a sanin cewa zan iya wannan b'arnan ba, sai da aka kwashi awa daya da rabi, sannan na koma gurin kwanciya ta, lokacin sunyi ihu har sun godewa Allah, sabida na rufe tagogin dakin. Sannan na koma nayi kwanciya ta a gefen Izmah, raina a b'ace.
Haka na kwana ina kallon duk wani motsinta, kiran sallah farko ya tadda Ni nayi alola da gabatar da sallar asuba, ina idarwa nayi mata wanka, sannan na nufi gurin amsar abincin. Anan me bada abincin take tambayar yan dakin mu.
"Me ya faru daku ne haka?"
Kallona suka yi tare da ganin yadda nake hada abincin mu. Sannan na dauki tire na jera.
Nazo zan wuce wasu kartin mata suka sha gabana, sunkuyar da kai Masu bamu abincin suka yi. Ajiye abincin nayi sanan na mikar da hannuna kashin hannun suka yi kara.
"Cikin girma da Arziki ku bani hanya na wuce, idan ba haka ba, al'adu zasu fiki daraja." Na fada ina murmushin mugunta.
"Toh me zai hana karamar yarinya!" Dariya nayi sannan na kalle su, rufeni suka yi da dukka gabaki daya dakin yayi shiru, sai karan sautin duka kawai yake tashi, a hankali na mike tare da ture su na dauki abincin mu, na fashe da dariya.
"Bana rena mutum, sabida ban san baiwar da Allah yayi mishi ba."
Nayi tafiya ta, kamar danyen nama haka suke ta zuɓewa a kasa.
"Kunga Yarinyar nan Shaidaniya ce! Idan kuka Cigaba da tab'a ta zaku fuskanci tashin hankali. Dan haka ku kyaleta horarriya ce, tasan me take yi." Inji wani me tsaron shashin bayin.
Zama nayi na kalle ta, sannan na bata abinci. Kallon yan dakin mu nayi suna ta ficewa a hankali kamar munafukai, sannan na kalle Izmah, nace mata.
"Meye ke damunki?"
Cikin zubda kwalla tace min.
"A cikin matan nan ne akwai wata me halitta biyu! Itace ta dauke min kimata, Ikram haka tayi ta saduwa dani tun bayan fitar ki, Don Allah ki nema min guba nasha na rantse da abin bauta gwara Firoz yaji labarin mutuwa ta akan yaji labarin abinda ya."
"Mutuwa ba ita bace karshen wasu abubuwan, ita din mafarin wasu abubuwan ce, a cikin matan da na daka bata cikin sune!". Kuka take tare da rike Ni tace min.
"Bata nan, daga wani daki take zuwa."
"Lallai sun tab'a me tsada, kuma zasu biya a furashi me tsadar biya, dan haka zan fita idan nafita zan kai kamar minti goma, zan dawo."
"Ina jin tsoro!"
"Kina tare dani, Ni kuma ina tare da Allah,tsoron me zaki ji? Kwantar da hankalinki, zanyi kome cikin tsarina." Na gaya mata bayan na gama bata abinci sannan na gyara mata kwanciya, na kalle su babu kowa a dakin. Fitowa nayi sannan, na fita abuna.
Tsayawa nayi a waje tare da jiran wani lokaci, ina nazarin abinda zan musu. Har na kwashe mintotin, sannan na kuma shiga cikin gidan, ina zuwa na sami kofar a rufe an bar mutum daya a waje, tun daga nan na fara cin ƙwallon Ubanta, har muka shiga cikin dakin. Sun bankare ta ita kuma Yar iskan tana tsaye da surar maza.
Rufe dakin nayi tare da jan wani katako na karya. "Hmmmm!" Nace musu, sannan na nufe su. Da farko sun zata zan ji tsoron karka su rufa min ne, ya sani tsayawa, nan kuwa gyara zaman katakon nayi.
Sai da na karya hannun da suka rike ta, ita kuma mata mazan nayi mata dukar kare dangi a gabanta, sannan na juya abuna, na kula da lafiyar Izmah, bude kofar aka yi.
Masu kula da shsshin mu ne suka shigo, nan suka tambaye ni, murmushi nayi sannan na nad'e hannuna a kirjina.
"Toh me zan ce muku? Kun barwa bayi damar suyi yadda suke so! Sannan a cikin gidan da mata suke kun bar mata maza tana rayuwa. Ku gyara ko na gyara kowa zama a cikin gidan nan."
Murmushi nayi sannan na juya na cigaba da abinda nake, ina gamawa na juya tare da kallon Izmah, fita aka yi da matan sam na manta da Amir Rahil.
~~~
Kallon su yayi tare da cewa.
"Hanyar yanzun Salsabila bata zo ba? Ku duba min ko tazo"
"Ran shi dad'e! Bata zo ba."
Kasa zama yayi ya kuma sake tuma tsalle can, zai kai musu duka. Kamar wanda ya tuna ya meda hannun sa baya. Tare da kallon su.
"Yallabai kaci abincin ka."
"Kaniyar Abincin! Da shegen kwalkwal dinka, maza wuce da fuskar shi kamar abinci. Yarinyar zaku."
"Amir ga Almirah Laylah tana zuwa."
"Kuce ta tafi bana son ganin ta."
Haka kuwa suka hanata shiga cikin gidan, ya daura daya akan daya, yana jiran Ikram, har rana ya fadi bata zo ba, sai yaji babu dad'i kawai ya share ba tare da ya kuma nuna damuwar shi ba.
Washi gari
Haka na tashi tare da kammala kome, sannan na rike hannun ta, muka nufi gidan Amir, tun a hanya take tambaya.
"Ina zamu?"
"Inda aka kawo ni aiki."
"Me yasa yau sai dani?"
"Karki damu, hakkin kula da lafiyar ki yana wuyana ne!"
Muna isa aka bude kofar, yana tsaye hannun shi goye a bayan shi. Kamar sakarai haka yazo ya tsaya min.
"Yanzun don Allah abinda kika yi ya dace, ki ajiye mutum kama na baki zo ba, gaskiya baki kyaita min ba."
Wallahi baya had'iye yawu, haka yake ta magana kamar na zubda kwalla, Izmah kuwa dariya ya bata. Hannun nakai bakin shi, tare da cewa.
"Ya isa haka!"
Lumshe idanun shi yayi tare da kallo na, gabaki daya ya tawo zai zube min a jiki tuni na kauce na bashi hanya ya zube a kasa.
"Ke mahaukaciyar ina ce? Amir Rahil kika sake ya fadi."
Mutumin ya faɗa da gudu rike da bulalar shi, sai da na bari ya tawo na mishi kwaf daya. Na gyara wuyana tare da cewa.
"Duk wanda ya ce zai min hawan kawara Ni kuma zan shayar dashi nono uwarshi!"
Mika mishi hannu nayi ya mike tare da kade jikin shi.
"Waye yace muku itace ta sani na fadi? Salsabila babu ruwanta da kome ko?"
Ya kalle ni yana murmushi, tare da wangale min baki, sha-sha-sha kawai. Na fada a raina, sam bai da wata Izza irinta me mulki, sakarai lamba daya shine wannan amma kuma son shi masu aikin shi suke, Ni kuma....
```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641```
#Mai_Dambu
[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021
*FURE cikin ƘAYA*
_CIGABAN DAULA BIYU_
BOOK TWO
_Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_
08
"Sakarai kawai" na fada da harshen swahili, juyawa wani dattijo yayi tare da cewa.
"Kema kin iya swahili ne?"
Kallon juna muka yi da Izmah sannan muka sake murmushi, muka ce mishi.
"Eh!"
Ai kuwa muka shiga hira dashi sama dama, duk da nikan ba sosai nake magana ba, amma Izmah kamar taga yan uwanta, haka suke hira. Kamar wani dolo ya tawo gurina ya tsaya.
Wangale min baki yayi irin hee (😬) zunzurutun bakin ciki kamar zan mutu, dan har da kai hannun shi kafadana yana dariya, da gudu ya jani muna nufi bayan gidan shi, kamar babban mutum haka suka shirya mishi gurin lambune, muna zuwa ya ture ni na zauna sannan ya zauna tare da cewa.
"Bani labarin garin ku"
Ina ƙoƙarin mikewa ya daura min kanshi akan cinyata, yana faɗin.
"Duk wanda kika ganshi anan yayi zama na amana da iyayena ne. Salsabila! Daga ganinki naji zuciyata ta kamu da kaunarki! Kuma naji ina kaunar na gaya miki halin da nake ciki.
Duk da kowa da yadda zai dauki rayuwar shi, amma rayuwata ta tana da muhimmanci a gurin kakanina.
A cikin dakin su mahaifina na, saura Autar su Abba ne yanzun Amirah Raziyana, babu kowa duk sun kare.
Sultan Mu'allim Abdulkarim, shine cikakken sunan kakana, yana da mata biyu, da Kwarkwarah daya. Sultanah Balkisu Ikram itace uwargidan shi, sai Amaryan shi Ummu Kulsum, matar tsohon sarkin nan garin ne, me suna Ahmad.
Yana da yara maza hudu, da mata biyu,
Yaran Balkisu sun Hada da Almustapha shine babba, Abubakar me bi mishi sai Aliyu, Abbana kenan, sai Autar su Raziyana.
Dakin Ummu Kulsum, akwai yara maza huɗu mata biyu, Sulaiman shine babban, sai Usman da Yahya, sai Isah.
Khalilah itace ke bin Isah da Nana A'ishah, dakin kwarkwarah shi kuwa akwai. Kamaliyah a yaki aka kawowa Sultan Mu'allim, tana da yara Biyu Abdullahi da Abdul Rahman, , Sultanah Balkisu Ikram, yar kasar Habasha ce, daga garin Minalik, mahaifinta sarki ne a can.
Dan haka..."
Barci ya cigaba da yi, naji zafin barcin shi gaskiya dan naso jin karshen Labarin shi, amma haka na hakura tare da dauke kai na..
Sakarai barci yayi abin shi fa, haka na gama duba ko ina na gidan ban ga kome ba, ina tsaye a bakin kofar fakon aka yi sanarwar Sultan Mu'allim ya zamo ganin jikan shi.
Durkusawa nayi tare da gaida shi. A hankali ya taka har gaban Amir Rahil, wanda yake barci saman kilishi, shafa kanshi yayi sannan ya kalle ni. Kai na a sunkuye.
"Yar nan! Don Allah Karki cutar dashi. Bai da laifi ko daya, naji ance tunda kika zo kike dukar shi, don Allah karki kuma ɗan nasan ba zai bari a hukunta ki ba, tunda har ya iya gayawa mutane baki mishi kome ba. Toh dan Allah karki mishi kome, idan turo ki aka yi Ni na dace da hukuncin ki ba bashi ba."
Cikin girmamawa na ce mishi.
"Allah ya taimake ka, wallahi babu kome a raina, ina haka ne dan na tuna mishi nauyin da yake kan shi, kayi hakuri ba zan kuma ba."
Mikewa kakan yayi sannan ya tawo gaba na,yana faɗin.
"Jikana amana ne a gare ki, gashi nan yana kwance kuma barci yake yi don Allah."
Sake matse hannun na nayi cikin wani irin yanayi, sannan nace mishi.
"Insha Allah!"
Sannan ya fita daga gidan, kallon Amir Rahil nayi kamar na rufe shi da duka. Haka nake ji, sabida ina zaman lafiya an kuma kara min nauyin shi. Lokacin Sallah yana yi na wuce nayi sannan nazo na amshi abinci na kira Izmah da ta sami Abokan hira sai hira suke abun su.
Zama nayi muka fara cin abincin, muna hira nan take gaya min tana son zama da Iyalan tsohon nan dan taga da tafi sakewa dashi, a duk lokacin da suke Yaren swahili. Kallon shi nayi sannan nace mishi.
"Kana jin me tace?"
Murmushi yayi sannan yace min.
Ai ba a wani waje bane a cikin gidan nan ne, Kinga wancan kofar gidan mu kenan, idan kema baki son zirga zirga zaki iya zama anan."
Murmushi nayi sannan nace mishi.
"BABU matsala, haka ma yayi."
Koda muka taso kayan Izmah na dauko musu, sannan na bata hakuri Ni zan zauna a gurin mu.
Alhamdulillahi, ki babu kome tana inda zata sami tsaro da kulawa, su kuma dakin mu, sabida ita nake d'aga musu kafa, domin ko jiya da ka rikice kuka ta fashe dashi tana ya da baya, alamar tana jin tsorona. Dan matuƙar raina ya b'aci Ni kaina har mamakin yadda nake juyewa nake.
A hankali kwanaki suke tafiya, wani irin shakuwa ya shiga tsakanin mu da Amir Rahil, kuma kamar mayye, indai ban zo ba, zai damu kowa har sai an duba ni. Dan da gaske na Fahimci wawan sona yake, Ni kuma a duniya babu wanda na tsana irin shi.
Dan haka muka yi ta shirya yadda zamu kashe shi, shakuwar da muka yi tasa shi matsawa lallai sai na kawo shi yawo. Dan haka cikin kasada, na dauke shi bayan na mishi kwalliya da shigar wata baiwa, muka fita.
Kamar zautacce haka ya rungume ni tare da sumbatar goshina.
"Ina son ki, domin ke daya kika bani farin cikin da nake bukata, don Allah ki taimake ni, kina dariya mana" (😬) ya wangale min baki.
Tsuke fuska nayi, sannan na wuce abuna, yana bina a baya, har muka shiga kasuwar, nan yai ta sayan kayan ciye ciye, yana mika min, har muka gama, wani guri da babu mutane, ya nuna min muke zauna.
"Salsabila! Me yasa baki dariya."
"Hmm" nayi tare da murmushin gefen baki, sannan nace mishi.
"Ban san me yasa fuskata ta wadattu da fusata ba, a koda yaushe ina jin ciwon abinda aka min. Na kashe min mijina, bayan nan dama bani da farin ciki ko bakin ciki sai rasa shi da nayi, babban burina na nufi SAMAIND na kashe wanda ya turo min aka kashe min Noman ranar auren mu."
Kura min ido yayi tare da sake abin da zai kai bakin shi. Idanun shi sunyi jajjur.
Tashi yayi tare da nufar hanyar da zai kai shi wani gurin.
Bin shi nayi tare da fisgo shi.
"Meye nufinka? Zaka janyo min magana ne? Ka tsaya na maida kai inda na dauko ka."
Kwace kan shi yayi tare da kallona yana zubda hawayen.
"Ki kyale ni, karki kuma tab'a ni"
Karan sautin zuwan abu naji dan haka na kwashe shi ya zube ƙasa, kallona yayi ya ga ina raba idanuna, hango wasu mutane nayi cikin duhu, su uku.
Da sauri na fisgo shi muka bar gurin da gudu, tare da shiga cikin Jama'a, kallona yake.
"Kinga abinda kika ja min ko?"
Marin wuyar shi nayi tare da juyawa na goye shi, muka shiga barin gurin da gudu kamar zamu tashi sama, ina saka kafana a kofar gidan shi, na sauke shi. Suka harbo min.wani karfe kamar ƙaya ya suke Ni ta baya sai da ya fito ta gaba. Haka na samu na shiga tare da rufe gidan, masu tsaro suka tawo da sauri.
"Ku shiga dashi cikin gidan" na fada ina layi, juyawa nayi tare da ɗaukar takobin ghaddafi, na fita, jini na zuba a kafadana, amma haka bai sani jin na hakura ba, komawa nayi inda aka fara abin.
Na zauna tare da ɗaukar abinda muka saya na fara ci a hankali, gani nayi sun kewaye Ni.
"Wato ke me taurin kai ko? Kin dawo"
"Waye ya harbe Ni da ƙwayar karfe?"
"Ba zamu gaya miki ba."
"Wannan shine mafi girman kuskuren da kuka aikata, daga kanku ya zama tarihi."
A fusace na juya muka fara yakan juna, a rayuwata na tsani kayan takaici, dan haka cikin fushi da bakin ciki, nayi ta kashe yan iska, aladu kawai. Ina gamawa na juya na koma gidan Amir Rahil.
Na ajiye takobin na koma gidan mu, ina zuwa.
Ina isa na samu duk sun yi barci, dan haka na cire kayana, na dauki kayan kulawar gaggawa da yake dakin na wanke ciwona, ina fitowa na samu an sace kayan jinin.
Ina kwance kawai sai ji nayi an watsa min ruwa, ina bude ido naga dakaru da manyan makamai, dan haka na mike a hankali. Haka suka tasa keya ta, zuwa gidan yari.
Bude idanu nayi tare da kallon inda nake, ban damu ba amma kuma kasar raina ina jin tsoron halin da na kuma jefa kai na, amma kuma nasan wancan sakaran zai nime ne ni.
Bayan an kawo ni sai ga wani mutum, yana nad'e da mayafi akan shi zuwa fuskar shi.
"Wacece ke? Meye na kawo ki masarautan mu da zaki kashe min mutane haka babu tausayi."
"Basu tausaya min bane, nima na shayar dasu nonan babar su." Na fada ina kallon shi.
"Hmm! Ku azabtar da ita yadda sai ta tuna ranar da ta gaya min magana ina Amir guda."
Bai bar