Showing 255001 words to 258000 words out of 274096 words
Chapter 86 - DAULA BIYU Complet Document .txt
kenan. Ya karaso da sauri jikina zai tab'a ni na ja baya, sake hawa gadon yayi naje garin matsawa na fadi daga gadon, na buge wani sunduki da kaina.
"Ikram!!!!" Ya kira suna na da mugun karfi.
Tare da isa gurin ya dauke ni, ganin yadda jini yake zuba yayi bala'in d'aga mishi hankali, kara rungume ni yayi tare da shafa bayana. Kwantar dani yayi, sannan ya nufi ban daki. Ya dauko ruwa da tsuma. Yana fitowa ya same ni a bakin kofar zan fita.
"Amma baki da hankali" ya dangwara da ruwan yayo kaina kamar zai dake ni domin ya d'aga hannun, aka bude kofar d'akin, Rahil ne ban san lokacin da na fada jikin shi ina kuka.
"Yayana don Allah Karku kai ni SAMAIND wallahi kashe ni Mehran zai yi"
Kallon Mehran yayi sannan yace min.
"Kiyi hakuri, duk abinda zai miki wata rana sai labari, Atta ya hana mu magana. Muje na gyara miki ciwon da kika ji."
Ganin yadda nake kuka tare da damukar Rahil, yasa baki daya kishi ya kuma turnike shi, ya zuciya tare da barin d'akin, haka Rahil ya taimaka min yayi min gyaran ciwon, sannan ya kawo min shayi nasha, kafin na kwanta. A hankali daren ya zame min dare mafi munin da bala'i a rayuwata, burina na Auri Mehran amma yanzun na zama mara amfani.
.......
Lokacin da ya isa masauki sai fushi da fada, tare da kwallo da kome, yana ganin ai cin amanar shi ake shi yasa nayiwa Rahil kyakyawan riko, dan haka sai ya dauki mata, a ranar dai haka muka kwana zuciyar kowa babu dad'i. Dake tafiyar sakamako ne za ayi.
.....
Ina ta jin motsin mutane ban san cewa, a dakin bane sai da na farka naga an kwashe kome nawa an fita dashi, a hankali Izama da Nimra suka taimaka min na nayi wanka, ina fitowa aka shirya min abun karyawa, ina gama cin abincin dakyar naci domin kamar magani nake jin shi.
.... Bayan na gama aka bani kaya na saka, sannan na fito. A hankali nake tafiya ina dafe bango har na isa babban shashin Sultan, inda kowa yake zaune. Kallon Amirah Laylah nayi tana murmushi, tare da mik'ewa ta taimaka min na zauna a daya daga cikin kujerun falon, ina haki.
"Toh Ikram Allah ya bada zaman lafiya."
Iya haka suka yi ta faɗa min, ban tab'a ganin abinda yayi min ciwo kamar yadda naga basu damu da ni ba, dan haka ana ce musu Mehran yana waje, suka rakoni baki dayan su, za a raka ni da kanshi ya sauko daga keken dokin yana kallon yadda nake tafiya ina niman Izmah ta rike ni, dake kofar cikin gidan akwai matakala,.jiri ne ya fara dibana. Dakyar nake sake kafana, ina kokuwa da numfashina.
Duhu ne ya Mamaye idanuna, kafin na kai kafana kasa naji kamar an tunkude ni ta baya. dukkan su kiran suna na suka yi da mugun karfi.
"Ikrammmmmm!" Shi kanshi bai san yadda aka yi ba, sai tsintar kan shi yayi ya tare ni tare da mun kyakyawan riko, jin yadda nake numfashi ga jikina yayi zafi ya sashi daukata tare da isa gurin iyayen na, yayi musu sallama da godiya har ya juya zai tafi dani Rahil yace mishi.
"Karka manta mariniya ce bata da uwa bata da Uba, bata da kowa A SAMAIND sai Allah. Masoyin gaskiya kokarin zama adali yake koda yake ita ai masoyiyyar gaskiya ce, duk wanda zata mu'amalance shi sai ta mishi adalci da zuciyarta tare da gangan jikin ta, dan haka ga Amana nan. Idan ka kula da ita Allah yana ganinka idan ka wulakantatta Allah yana ganinka. Muna sonta muka bar maka ita ba tare da duba waye kai ba, sai dan duba meye take so.
Iya mu biyu muka ragewa kakar mu idan ba zaka iya zama da ita ba, ka dawo mana da ita kar ciwon zuciya ya kashe mana ita bayan bamu more ta ba."
A karon farko da yaji kunya ya kama shi, sunkuyar da kai yayi sannan yace mishi.
"Insha Allah zan rike amanar da ka bani, kayi hakuri da abinda na aikata laifukan da nayi mata, amma ba zan iya hana zuciyata kishin abinda nake masa so sama da kome ba, iya wannan zan gaya maka gaskiya."
Daga haka ya juya tare da sauka daga matakalar ya nufi cikin keken dokin dani, muka bar masarautan.
_Yadda ta ji dadin namiji ne ta kawo maka kanta? Ni kaina nasan ta manta da kwakular da nake mata_
Juya min baya yayi tare da kallon waje, yana ji kamar zuciyar shi zata buga. Juyawa yayi yaga yadda nake zubda kwalla. Duk sai jikin shi yayi masifar sanyi. Shafa kaina yayi cikin nutsuwa yace min.
"Me yasa kika zab'i zubda kimar ki sama da kome? Kinsan yadda nake burin zama da ke? Ina miki wani irin kauna ce me wuyar fassaruwa. Kaunar da nake miki gaskiya ce ban tab'a hadaki da.."
"Mehran kaunar da kake min karya ce, baka kaunata baka bukata na a rayuwar ka, idan da kana kaunata ba zaka tozartani daga auren mu ba, amma ka zab'i cilla rayuwata cikin ukuba."
Fusata yayi tare da d'ago ni zaune, ya shiga gaya min magana marasa dad'i, tare da goranta min abinda a ka gaya mishi..
"Ni ba karuwa bace, idan har dan ya kwana dani a daki daya a gado daya shine karuwanci toh ai kai ma kayi haka dani ko ka manta ne? In tuna maka" na tambaye shi ina zubda hawayen bakin ciki.
Marin bakina yayi tare da shake min wuya.
"Ni zaki tsinkawa mutunci kiyi laifi ba zaki bani hakuri ba , sannan ki nuna min ai ba sabon abu bane a gurinki."
"Eh na fada karya na maka na gaji zaka kashe ni da rayuwata ta, meye nayi maka da zafi da ka zab'i cilla ni cikin damuwa?" Ban san meke damun shi ba, domin kamar mara hankali ya koma min tare da marin bakina da fuskana, sai da yaga na fara tarin jini,. yana fita ta hanci da bakina ya sa shi barin abinda yake min. Rungumo ni yayi tare da cewa.
"Matukar kika ce zaki mai da min raddi zaki yi kuka ban tab'a d'aga hannu akan mace ba amma nayi a kanki. Kun cuce ni wallahi kuma ban yafe miki ba."
Haka yayi ta niman magani na, har ya gaji sannan yayi magana aka tsaya, dakyar aka samo maganin a gurin Izamah.
Haka muka Cigaba da tafiya har dare, sannan muka yadda zango sabida dare, tunda ya gyara min kwanciya, yasa kai zai. Ban kula shi ba kawai abinda na sani zan gyara jikina, daukar abin gyaran nayi na fita daga tantin yana kallona, na nufi dajin, bin bayana yayi tare da tsayawa a kaina na wanke jikina tare da saka sabon abin tare jinin, sannan ya haƙa rami ya binne wanda na cire, kafin ya saka ni a gaba zamu bar gurin. Sai ji muka yi an zagaye mu.
"Mun zo daukar Amaryarka ce ka bamu ita zamu dawo maka da ita idan Maigidan mu yayi abinda zai iya da ita, idan kuma kaki zamu maka rubdugu"
"Nayi muku alqawarin duk wanda ya tab'a ta ba tare da na yanke hannun shi ba, toh wallahi yayi tafiyar shi da ita, babu kome na bar muku ita, idan kuma na sare hannayen ku zan kashe ku baki daya."
Zare takobin shi yayi tare da kallon su, yace musu.
"Bismillah;"
Aikuwa suka kawo min cafka, mara imani kamar ba yan adam ba, haka yayi ta sare hannun su, sai da yayi musu illa. Kafin aka sami wanda ya buga mishi itacce a keyar shi, ya fad'i. Yana kallon mutumin ya kai hannun shi ya dauke ni bayan ya fesa min wani abu na zube a jikin shi.
Lumshe idanun shi yayi sannan ya bude a hankali ya hango mutumin yana tafiya a cikin dajin, sake lumshe idanun shi yayi ya cigaba da hango. Cikin wani irin zafin nama ya mike da mugun gudu, yayi bayan mutumin, kafin ya fahimci abinda yake faruwa a bayan shi Mehran ya buga shi da kasa,, wasu mutanen biyu suka kuma bayyana tare da ɗaukata da gudu .
Haka suka yi ta bashi wahala, har suka b'ace mishi, sakamakon watsa mishi kasa da suka yi.
Murmushi Abrad yayi tare da kallon kyakyawan fuskar ta wanda yake cike gwanin ban sha'awa, tayi kyau fatar ta ta murje, sumbatar bakinta yayi tare da kai hannun shi saman kanta. Yana maida gashinta baya,.
Ihun mutanen shi yaji dan haka da sauri ya, saka wuka ya yaga kayan jikinta bayan yayi arba da kirjinta, wani irin dadi ne ya kama shi, jin Mehran yana tunkaro shi yasa shi yaga tantin ya fita ta baya, ki babu kome ya kuma cusa mishi zargin Ikram.
Lokacin da ya shigo ya samu babu kome a jikina kayan duk an yaga, cire rigar shi yayi na alkyaba. Ya lulluba mata. Yana jin kamar zuciyar shi zata buga. Haka ya dauke ta ya fito da ita, tare da komawa inda suka yadda zango.
Duk abinda ya faru yasan shirin Abrad ne, amma bai tab'a kawowa zai bi matar auren shi ba, dan haka ya saka a ranshi duk ranar da ya kama Abrad zai mishi kisar da ba a tab'awa wani mahaluki ba.
A tantin ya kwana yana kallon yadda take barci, cikin nutsuwa da kamala, har gari ya waye. A hankali na bude idanuna na same ni a jikin Mehran mun makale juna,kallon shi nayi yana barci cikin nutsuwa da alamun ma, tunda yayi Sallah asuba ya dawo kusa dani, kewar shi da kaunar shine suka kuma kama zuciyata gyara kwanciya nayi a jihar kin shi. Dake jiya bai rintsa ba, sai gashi shima ya gyara min kwanciya na. Ajiyar zuciya na sauke. Jin na jika jikina yasa ni tashi tare da hayewa gefe, shima kuma kamar a mafarki ya tashi, yana kallona. Kamar zanyi kuka nace mishi.
"Zan yi wanka da gyara jikina."
Wurga min kayayyakina yayi muka fita, Nimra da Izmah suka tawo tare da amsar kayan muka nufi wani koramar, sai da aka gama duba gurin tsaf sannan dakarun suka koma, ina kallon shi ya cire kayan shi ya shiga ruwan ya zauna.
A hankali na cire kayan jikina da ya yage, sannan na koma gefe na wanke jikina, kafin na zauna a cikin ruwan, nutso yayi tare da zuwa inda nake, kallon shi nayi na dauke kaina,.ina goga sabulu a jikina, fisgo ni yayi muka shiga cikin ruwan sosai, inda kafana bai isa cikin ruwan ba, rungume ni yayi yana shafa fuskana, tare da nutsar da kanmu cikin ruwan muna kallon juna. A hankali ya d'ago ni sannan ya shafa bayana, kurawa kirjina ido yayi sannan ya kira kan shi a tsakanin su, yana me jin wani irin yanayi yana ratsa shi. Ni dai nawa ido. Har muka gama wankan.....
[5/24, 7:22 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat
Book3
_Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_
14....
"Yaushe zaki gama jinin?" Ya tambaye ni tare da d'aga kan shi a kirjina, shiru nayi mishi ina me Cigaba da wasa da gargasa jikin shi. Matse ni yayi sai da nayi kara sannan ya kalle ni.
"Dan iska kika mai dani?"
Nan ma shiru nayi mishi, ya kuma jin haushi sama da ta Farko. "Ina magana kin mai dani sakarai ko?" Kokarin kwace kaina nake ya kuma matse ni sosai.
"Meye nayi miki kike azabtar da ruhina haka?" Kwalla ne suka cika min ban san lokacin da dariya ya kwace min, tare da kallon shi, sannan na janye daga jikin shi zan fice daga ruwan,
Rigani fitowa tare da kwashe kayana ya rike.
"Tambayar ki nake?" Murmushi nayi tare da juya bayana na cigaba da wasa da ruwan, indai nice yanzun muka fara, da yaga ba zan mishi yadda yake so ba, ya ajiye min kayan ya kawo min kayan na sauya sannan na fito na gyara jikina muka dawo sansanin mu. Har muka karya muka bar gurin niman abinda zai min tijara yake ban bashi kofa ba.
Mun isa SAMAIND da kusan azhar, dan haka kafin mu shiga garin aka shelata akan Sultan MEHRAN ya dawo da Amaryan shi, haka yasa aka tare mu sosai. Ana bikin murnar har muka shiga cikin masarautan, kowa jira yake yaga Amaryan.
A kofar shiga gidan aka tsayar da keken dokin da muke ciki, ya rigani fita sannan, na fito tare da taimakon shi ya rike min hannuna. Muka nufi cikin gidan. Duk Kwarkwarorin shi sun zaku su ga wacece, ganin Izmah da Nimra yasa fahimtar Ikram ce.
"Wato auro Ikram yayi bayan muna jiran shi?" Inji Jasrah, ta faɗa a sanyayye, domin abin ya bata mamaki.
Babban shashin Sultanah Fazilatul nisa na da shi aka ware min bayan an kawo kayan da yake mallakina anata jera su, har dare sannan aka gama, daga nan muka shige cikin ɗakin Ni da bayina, nuna musu dakin su kayi dan basu da yawa, su uku ne Izama da Nimra da kuma Ruwaida.
Kafin na shiga ban daki nayi wanka tare da gyara jikina dan nasan gobe zan tsarkaka.
Kwanciya nayi a fankacecen gadon da aka mallaka min ni daya, ina tuna irin kaunar da ake min a cikin dangina, kwalla ce ya zubo min, haka ka kwana ina kuka. Sai goshin asuba Bauchi ya sauke ni.
***
Lokacin da ya shiga turakar shi, bin bayan shi Azizatul tayi cikin kuka da bakin kishi.
"Me yasa mu ka ki auren mu? Wato sai Ikram ko?"
Ta faɗa da karfi, hawaye na zuba daga idanunta. Tare da kafe shi da idanunta, duk matan da suke cikin masarautan bata kishin su, bata jin zasu sami Mehran, Amma a duk lokacin da ta tuna da Ikram itace Muradin Mehran sai wani irin tsoro da shakku ya kamata, Uwa uba duk mazan da suke tare da ita haka suke tare da ikram. Idan d'an uwan ta, babu macen da yake so sama da Ikram, Nawwas shima haka,.haka ma Norman shima Ikram duk mazan da suka shiga rayuwarta Ikram sai ta kwace mata shi. Yau ga Mehran da ya shigo rayuwarta ta samu Ikram ta kwashe casa'in da tara na soyayyar shi. Sai ka shi daya ta bar musu, shima bata da yakinin zata samu. Fita tayi daga dakin ta na jin tabbas zata dauki mataki.
Kayan shi ya fara kokarin ragewa, bai kulata ba ya shiga ban daki. Bayan ya haɗa ruwan wanka, sannan ya shiga cikin ruwan, ya zauna yana tuna wanka da suke yi yau da safe, ji yayi baki daya kome na shi ya tsaya cak,ya shiga zuba ruwan a ko ina na jikin shi musamman inda ya lura ikram tayi ta tab'a mishi, wato kirjin shi zuwa kan tarin surar jikin shi da suke murɗe, sai yau ya kuma tabbatar da tana mugun son wannan surar jikin shi. Murmushi yayi sannan ya gyara zaman shi cikin ruwan, kamar wanda yake tare da ita, sai mik'ewa yayi tare da. Daureye jikin shi ya fito.
Saka jallabiyar shi yayi tare da nufar d'akinta, taba kwance ya shigo mata kai. Dake ta rage hasken d'akinta tana kallon shi, ya hauro mata gado, janye rigar shi yayi tare da kwanciya yana kallon inda nake kwance.
"Zoki min tausa!"
"Kaje kamilan matan da ka tara su maka ni shara ce" d'agowa yayi tare da kallona.
"Ki zo ki min tausa!" Ya faɗa a sanyayye, domin abinda na Fahimta ya gaji, ina kyautatta zaton ko abinci bai ci ba, amma yazo niman magana.
Juya mishi baya nayi tare da cewa.
"Nayi alƙawarin da kaina ba zan tab'a maka kome ba."
Fisgo ni yayi tare da kallon fuskana.
"Duk sauran matan basa iya min magana na rashin ɗa'a amma ke, kin masifar rena ni, dan kin saba masu kananun azzakari suna goga miki a gabanki shine bari ki min rashin kunya."
"Toh Me babban azzakari an hanaka goga baka ne? Ni ban zata ma kai cikakken namiji bane sai dai ina ganin ka cikin suffar maza." Sake baki yayi yana kallona, tare da kasa min kome.
"Ni kika gayawa magana Ikram?"
"A'a magana ce fa idan kasan na fada baka san na maidawa ba." Na fada ina me juya mishi baya,
"Ni kika gayawa magana?"
"Mehran ni bayan gaya maka magana ba, kawai kuskuren fahimta Ce."
"Ikram!" Ya mike tare da saka kayan shi zai fita, dan ranshi yayi masifar b'aci, ko a jikina gyara kwanciya nayi, tare da cewa.
" Sauka lafiya"
Tunda ya saka kai ya fita, ya hadu da Azizatul Nissah, kallon shi tayi tare da cewa.
"Sultan MEHRAN!" Wani irin kallon banza ya watsa mata," sannan ya wuce.
....
Washi gari.
Bayan na tashi ni dasu Izmah muka shiga gyara d'akin, bayan mun gama muka saka turarukan wuta, masu shegen kyau da dad'i. Sannan nima na dauko kayan gyaran jikina, sabida hailata da nake ganin Yau zata dauke. Cire riga nayi tare da daure kirjina da wani mayafi, suka shiga shafa min. Abun gyara jikin. Tare da da goga min A bayana, a hankali suna min hira, duk da ina sauraron su, amma hankali na, yana ha Mehran da yau bai shigo ba. Duk