Showing 243001 words to 246000 words out of 274096 words
Chapter 82 - DAULA BIYU Complet Document .txt
damuwa ta nufi hanyar barin gurin, kallon Fudail tayi sannan tace mishi.
"Yaki saurarona, ban san me haka yake nufi ba, dama haka yake da kafiya?"
"Rashin Ikram ce ya kuma mai dashi zuwa haka"
"Tana ina ne yanzun?"ta tambaye shi.
"Tana can Merocco, ana shirin bikinta da Amir Rahil, dan uwanta ne" ya bata amsa,
"Toh amma haka zamu zuba ido muna kallon shi babu me iya tankwara shi akan abinda yake aikatawa? Ni yanzun idan nace zan tafi can, zai yi wuya ya barni na tafi amma don Allah kayi wani abu, sannan a kaiwa Anneh bayinta domin jikin girma da damuwa zai mata yawa, idan aka kai mata mutane tana jin motsin su zata rage damuwa."
Gyada mata kai yayi sannan yace mata.
"Toh ya zamu yi da Mehran idan ya fahimci mun kai mata bayi?"
"Karka damu, zan gyara kome Insha Allah. Sannan ka sami lokaci ka bani labarin Ikram, tayu na dauki wani abu daga cikin halayyar ta."
Gyada mata kai yayi sannan suka yi sakayi sallama, ta bar gurin. Cike da gamsuwa. Idan baka iya kuka ba aka ce uwarka ce bata mutu ba, dan haka Sawda tayi amfani da wasu dabi'a tare da bin bayan Mahaifiyarshi domin samun kusanci da ita.
Tun daga ranar ta maida gurin shi gurin hirar ta, dukda tana yawan mishi shirme haka yasa shi jin zai iya sawa a dawo da Mahaifiyar shi, tunda itama Sawda tayi kokarin ganin ya fahimci gaskiya, sanan itama tana kokarin zuwa har inda Sultanah Fazilatul nisa take, tana zama da ita.
~~
Kallon kakan shi yayi wanda ya haifi Mahaifiyarshi, kafin ya shiga wasa da kofin shayin da aka bashi ya cigaba da cewa.
"Insha Allah zan yi yadda kace, sai dai zuciyata ba zata ji dadi ba,"
"Ka gwada Rahil zaka sami nutsuwa, kuma itama zata girmama al'amarin ka, zata kuma gane kai mutum ne me nagarta, amma idan ka nuna mata kai Kanka kake so zayi wuya baka samu tangarda da ita ba! Amma kayi nazari da kai."
Kai kofin shayin yayi sannan ya kurba, mik'ewa yayi tare da cewa.
"Zan koma"
A hankali ya mike tare da barin gidan kakan shi, wani irin tausayi ya bashi, yana son Ikram amma kuma shi a nashi tunanin ya hakura da ita, badan kome ba, sai dan yadda tazo jiya ta gaishe da kakan da ya kalle ta sannan tace mata.
"Bilqisul Ikram! Ya batun shirye shiryen bikin ku, naga anata tura sakon gayyata"
Matse hannun ta, tayi tare da sunkuyar da kanta sannan tace mishi.
"Ana kan shirin."
Murmushi yayi sannan yace mata.
"Ke baki shirya bane"
Matse hannunta tayi kamar zata karya shi.
"Ina kai"
Kura mata ido yayi sai ya fahimci bata son maganar auren ne baki daya, dan haka ya jefeta da tambayar da ta sata d'ago kai.
"Shin ko kina da wanda kike so ne? Bamu sani ba"
Da sauri ta d'ago kai tana kallon shi sannan ta kuma maida kanta kasa,.kwallar da take kokarin dannewa ne ya shiga sauko mata, a hankali ta saka bayan hannunta ta goge. Murmushi irinta manya yayi mata sannan yace mata.
"Share hawayen ki, kinji kiyi hakuri da abinda muka zab'a miki,.Insha Allah zaki yi farin ciki."
Gyada kai tayi tare da mik'ewa zata bar falon, duk sai yaji babu dad'i musamman yadda ta kasa rike kukanta, dan haka yake ji ba mata adalci ba, dan haka yake ganin koda anyi auren zasu ta azabtar da juna ne ta hanyar amfani da k'iyayyar juna, shafa gemun shi yayi, dan yasan auren kan babu fashi. Kamar anyi an gama ne ma.
.......
Kallon sakon gayyatar Masarautan SAMAIND yayi, sannan ya ajiye shi a gefe kafin yace.
"Zanje da kaina naga meye Mehran ya fini dashi"
Dan haka ya mike tare da nufar cikin gidan, yana shiga ya wuce dakin kakan shi wato Sultan Mu'allim, zama yayi sannan yace mishi.
"Ka tura na ko ina amma ni zan kai na SAMAIND tunda ta zauna a gurin Sarkin Daular, ka ga kenan zamu gayyace shi."
Murmushi yayi sannan yace mishi.
"Allah ya jikan Iyayen ka, ina son yadda kake nuna jarumtar nan,.dan haka ka shirya gobe Insha Allah ka kai mishi!"
Gyada kai yayi sannan ya mike tare da yin sallamawa kakan, dakin Ikram ya nufa, ya same ta ta cusa kanta a tsakanin cinyoyinta, tayi wani mugun kyau da cika, shi kanshi sai da yaji a aran shi ya dauke ta ya boye ta shi dayan shi. Sai kace Yar tsana, birkitotta yayi yana sumbatar goshinta.
A hankali ya saukar da kanshi zuwa wuyarta.
"Ikram me zan gayawa Saurayin ki domin zan kai mishi sakon gayyata na bikin mu."
Ban san lokacin da na d'ago da mugun sauri ba, nace.
"Mehran? Gurin shi zaka?" Sharr hawaye ya fara zuba, kamar yadda nake tsammanin, kasa tabuka kome nayi, na lumshe idanuna..ina jin wani irin kuka yana zuwa min, shi kuwa abinda yake son gani kenan, dan haka ya zame ni cikin lumana ya fara jagwalgwala ni, rike hannun shi nayi tare da cewa.
"Don Allah,.karka min haka duk tsawon lokacin da na kare kaina, bai isa ba sai lokacin da ya rage taki kadan kace zaka kutsa min."
Janye jikin shi yayi sannan ya sauka a gadon, tare da fita zuwa dakin Sultanah Balkisu Ikram, sun jima suna hira kafin yayi mata sallama. Tunda ya fita nake kuka. Domin yau nake jin wani irin kewar Mehran, ban tab'a sanin cewa na haukace akan Mehran ba sai da yace min zai tafi gurin shi, naji kamar na cire zuciyata na bashi ya kai mishi, haka Izmah da Nimra suka shigo min itama kallona take, tare da cewa.
"Naji wai Amir Rahil zai tafi SAMAIND, amma zan bashi sako ya kaiwa Fudail."
Gyada mata kai nayi, sannan na juya musu baya na kwanta ina ajiyar zuciya, har barci ya dauke ni, ban farka ba sai da dare ya raba sannan na nufi ban daki nayi alola, sannan nazo na gabatar da sallar nafilla, na jima i a gayawa Allah kuka na, ina kuma niman a gaji a gare shi, kwallar da nake danne su, suka zuba min, tabbas so masifa
[5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat
Book3
_Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_
8...
"Ya Allah kai ne ka jarabce ni da Kaunar Mehran ya Allah ka cire min kaunar shi a raina na huta" na fada cikin kuka da shashekar kuka, a hankali wani irin zazzaɓi ya rufe ni, kafin wani lokaci na fita hayacina.
Shigowar Izmah da Nimra yasa aka fahimci halin da nake ciki har ta kai da an nimo masu kula da lafiyar mutanen masarautan.
Haka suka kwana a kaina, Dan koda Rahil ya shigo yaga halin da nake ciki bai hana shi tafiya ba, dan ya san akan Mehran ne, kuma babu fashi akan auren anyi an gama. Sallama yayi musu ya kad'a raƙumin shi dan yace ba zai shiga a matsayin me muƙami ba, zai yi tafiya ce Irinta Sadaukan maza.
Sai dai dukda haka yayi tafiyar ce cikin zullumi da damuwa, domin saura kwanaki ƙalilan bikin su, kuma baya Mantawa a watanin baya Ikram da bakinta take cewa.
"Ba zan ki aurenka ba, amma Ni kaina nasan cewa mutuwa tace take tunkaro ni, ba zan iya furtawa ba, amma kuma ba zan tab'a yarda na zama mallakar wani ba. A duk lokacin da na Fahimci tazarar da take tsakanin mu sai naji a raina kamar kuskuren nayi aka jarabce ni da samun ahalina me yasa kika bayyana a lokacin da nake shirin zama a Inuwar shi, tabbas mutuwata itace fansa ga kaunar da nake mishi."
Lumshe idanun shi yayi wanda yake rufe cikin mayafi me kyau da tsari. Lumshe idanun shi yayi ya bude shi. Murmushi yayi me kyau sannan ya cigaba da tafiya yana ratsa hamada da sahara.
"Ba aikata kuskure bane laifi, maimaita kuskuren shine babban laifi, Ya Allah ka gafarta mana kura kuran mu," ya faɗa yana me shan ruwan shi da yake goran shi ya sha. Ya kuma zaburar Raƙumin shi.
~~
Kallon Sultan Mu'allim da Amir Sulaiman da Wazir. Me kula da lafiyar ta yayi sannan ya sunkuyar da kanshi yace musu.
"Allah ya taimaki Sultan, Amirah Ikram tana fama da damuwa ne, sannan zucuyarta bugun shi yayi kasa, idan da hali a rage takura mata, domin tana bukatar nutsu a daina takura mata, sannan a daina barin ta ita daya tana zaman kaɗaici haka ma yana taimakawa gurin shiga damuwa."
Shiru yayi sannan ya cigaba da cewa.
"Na gama duba ta" ya faɗa tare da musu sallama zai tafi. Rakiya Amir Sulaiman yayi mishi. Zama Sultan Mu'allim yayi tare da kallon yadda fuskarta yayi wani irin fayau. Shafa kwantaccen gashin goshinta yayi yana tausayin ta, duk da Wazir ya gaya mishi matsalar Ikram amma gani yake kamar idan anyi bikin su da Rahil zata hakura, abinda bai sani ba kuwa ashe ciwo cinta yake kuma dalilin son ransu. Gani suke kamar duk wani karfin mulki yana tare da Ikram shi yasa basu son rabuwa da ita, Kuma idan tana tare dasu. Shi yasa yaki sauraron kowa kan Mehran haka zata hakuri ayi bikin da Rahil.
~~
Oman.
"Baku sami labarin daga SAMAIND ba?" Abrad ya bukaci jin bayani daga bakin wani na hannun damar shi bayan kashe Nawwas, me suna Ukshe.
"Eh an sami labarin an ga gawan Nawwas, kuma sun gama binciken yadda gawan ya mutu, sai kuma batun Amirah Azizatul Nissah, Mehran ya amshi cikin jikinta, bayan haka tayi nasarar sashi ya kori Mahaifiyar shi daga cikin masarautan. Sai batu na gaba bikin Amirah Ikram da za ayi da Amir Rahil, nan da kwanaki goma sha biyu."
Murmushin gefen baki yayi tare da kallon shi, yace.
"Ukshe ina ganin ya kamata a sace min Ikram ranar daurin aurenta a daren da ake shagalin a daren nake son nayi tarayya da ita, yadda zata gane nayiwa maza Zarra"
Murmushi Ukshe yayi sannan yace mishi.
"Nasan ka kuma nasan zaka iya, shi yasa nake farin cikin kasancewa ta a kusa da kai, Sultan Abrad indai Ikram zata gyara daren ka da Ikram ai babu wani uban da zai hana ayi wannan badakalar."
Murmushi yayi tare da gyada kai, domin kuwa yana jin a ran shi an gama mishi kome tunda yaji labarin auren, sannan ya kalli Ukshe yace mishi.
" Yarinyar daban ce ga sauran matan ko Kanwar Mahaifiyar ta bata kaita haduwa ba, Ikram haduwa ce ita kanta kome ce."
Murmushi yayi sannan ya cigaba da cewa.
"Zanyi fatan ba iya dare zan b'ata ba dararrakin rayuwata zan b'ata ina shiga ina fita a jikin Yarinyar nan, so nake nayi ta nutso a jikinta ina jin Yaren da ban tab'a ji ba."
Yana tuno lokacin da yake tare da ita a matsayin baiwar shi, idan ya tuna yan madaidaita nonuwarta sai yaji kome ya tsaya mishi gaskiya yarinyar karshe ce, kasanta da yayi yunkurin cusa hannun shi cikinta kasawa yayi karshe itama taki yarda, balle kuma yanzun da take Jinin Sarauta, Sai dai ai Noman ya aureta ko bai kwanta da ita bane? Zare idanu yayi lokacin da yake ji a ranshi babu abinda noman yayi mata tabbas, kuma a haduwar su tabiyu bai ga alamar ta tab'a kwanciya da namiji ba, indai haka ne toh akwai wani abu a lullube da ita, lallai kuwa dole idan ya isa gurin daurin auren ya saka a sato mishi ita yayi daren da yake fata da ita. Idan ba haka ba, tabbas zai iya yakar daular ba tare da ya fahimci abinda suka mishi ba indai akan ikram ce toh kowa ma zai kashe.
Duk wanda ya tsaya mishi a gaba zai kawar da shi, ita kanta idan zata kawo mishi cikas, zai iya daukar mugun mataki akan ta, balle kuma wani banza can zai kashe kowa indan akan Ikram ne, zai iya shirya kome dan ya mallake ta. Ba iya ita ba kome ma indai mallakarta ce.
Murmushi yayi sannan yayi gyaran murya yace.
"Ukshe ka gyara min gidana da yake wajen masarautan nan za a kawo min ita "
"Toh an gama Sultan!" Ya juya tare da barin d'akin, yana murmushin jin dadi, dan shima Ukshe bakin Shaidani ne, a gurin.
~~
Alamura sun kuma tabarbarewa a Samaind, domin an sami ɓullowar Farin suna ta cinye abincin mutanen garin, tare da lalata musu amfanin gona, shiru yayi yana kallon yadda kowa yake magana, amma cikanku bai baice ba.
"Farin nan kashe mutane suke idan sun je kare abincin gonan su. Kuma Sultan Mehran baka ce kome ba."
Sai lokacin ya d'ago kan shi, yana kallon su, kafin ya sauke ajiyar zuciya yace musu.
"Toh me zanyi musu? Ko nine zan kora musu farin. Abinda zai faru kawai a tabbatar an dakatar da mutane su zauna a gidajen su, sannan su tabbatar da sunyi rike kayan abincin Insha Allah duk tsanani yana tare da sauki, Insha ALLAH, Ubangiji zai duba al'amarin su." Yana fadar haka ya mike tare barin fadar, yana fita suka dasa gulmar shi da kunshe tsarin shi, dan haka yana fita ya kalli Fudail.
"Muna da mutane a cikin gari da makotan mu, dan haka kayi ƙoƙarin gano mutane masu amana ka dibi abinci ayi ta rabawa mutane na yarda da kai ya sani cewa haka, kayi aikin cikin kulawa bana son damuwa kuma bana son a nuna muna da hannu a cikin al'amarin"
Gyada mishi kai yayi tare da cewa.
"Toh Sultan Mehran."
Tunda ya isa yake baza idanun shi ta inda zai ga Sawda, har ya shiga turakar shi, tarar da Azizatul Nissah yayi taci Uban kwalliyar, kallonta yayi sannan yace mata.
"Tashi ki fita bana bukatar ganin ki," ya gaya mata haka domin har yanzun yana jin zafin ta da abinda tayi mishi.
"Kayi hakuri ba zan kuma maganar Ikram ba, kayi hakuri nabi Allah na bika duk abinda kace zanyi Sultan Mehran." Ganin yadda take kuka ne ya sa shi jin kamar kome ya wuce d'agota yayi tare da cewa.
"Karki kuma min abinda kika min na gaya miki, kuma ya wuce amma ki turo min Sawda."
A kidime ta kalle shi tana faɗin.
"Sultan MEHRAN baka hakura bane."
"A'a na hakura ina son ganawa da ita ne " fashewa ta yi da kuka tare da mik'ewa ta saka kai zata fita.
"Ke zo nan ya kirata." Jikinta yana rawa ta dawo.
"Ki share kwallarki, bana son na kuma jin Kinyi kuka. Maza share kwalla Uwar Yarima" gyada kai tayi sannan ta share kwallarta kafin ta fita, murmushi tayi sannan ta tura aka kira mata Sawda, zama tayi bayan sunyi musayan murmushi sannan tacewa Sawda.
" Ki sha ruwa sannan Sultan MEHRAN yana gayyatar ki dakin shi, da Fatan babu wani wanda ya tab'a shigarki."
"Ai tsadar da muka dashi ya wuce Musami tarbiyyar namiji, Mace ta rene ni, kuma cikin gidan Sarauta, dan haka mun san yadda ake rike kimar mace, bama wasa da darajar mu."
Ta fadi haka tana me mik'ewa zata bar falon, "Ya kamar kinji haushin abinda na tambaya."
"Ai nasan koshi Sultan Aamaan Mehran ba zai yi min wannan tambayar ba, balle kuma ke dan ni na taso inda aka samu tarbiyya ne ba inda aka maida mata kamar dabobbi ba"
Taji haushin kalaman Sawda, amma dake ta iya makirci mik'ewa tayi tare da mata jagora har Turakar Sultan Mehran. Suna shiga tace mata.
"Allah ya baki hakuri, bazan kuma miki magana ba, kuma ai cewa yayi zaku gana da kike gaya min abinda ya shafi rayuwar ki, ban tambaye ki, ban sha'awan na sam me ya tab'a faruwa dake, idan ma Fyade aka miki ai bai dace ki ce zaki gaya min ba, wannan sirrin kice"
Shiru tayi tana kallon SULTAN Mehran, sunkuyar da kai tayi murmushi Sawda tayi sannan tace mata.
"Karki damu, idan ma maza dubu suka kwana dani ba shine damuwar ba, kasami wanda zai yarda da kai ma arziki ne, ke kika san abinda kike kullawa na sharri da Alkhairi, algunguma kawai."
Cikin jin haushi ta kaiwa Sawda duka, aikuwa fada ya kaure a tsakanin su,, daka musu tsawa yayi da sauri suka rabu.
"Ku fita min a d'akina" ya fada da mugun karfi, babu musu suka juya tare da barin d'akin shi.
Dafe goshinsa yayi tare da jin bala'in ciwon kai. Sabida damuwar mutanen shi da matan da suke kasar shi. Karshe da kan shi ya sauka ya nimo Mahlika.
Ya umarce ta ta kawo mishi shayi yana jiran ta, kamar zata yi kuka haka ta tashi ta girka mishi ruwan zafi. Ta kai mishi har dakin, yau haka kawai ya tashi da wani irin fitinnnen bukatar mace, shi yasa yaso kasancewa da Sawda ita kuma Azizatul ta janyo musu rigima.
Tana tsaye kamar wata dogariya, yace mata.
"Ki shiga ban daki kiyi wanka" a hankali ta wuce tare da shiga, ya jima yana nazarin abubuwan dayawa a ran shi, kafin ya gama sha ya rage haske dakin shi, yana zaune a gurin ta fito tana goge jikinta da gashin kanta.
"Barshi kizo kiyi min tausa."
A hankali ta ajiye mayafin da take goge kanta dashi, ta haura gadon, rubda ciki yayi, ta haura bayan shi. A hankali take matsa mishi jiki, musamman wuyar shi zuwa kafad'ar shi,. Ruwan gashin kanta yana diga a bayan shi, yana jin saukar ruwan har cikin kanshi, ƙwaƙwalwar shi da zuciyar shi suka fara bashi Ina ma Ikram ce, wani irin yanayi zai samu kanshi. Gabaki daya yaji duniyar shi ta sauya, dan autan wandon shi kuwa sai zillo take tana ihu. Mika yayi tare da juyawa da ita. Saman shi