Showing 33001 words to 36000 words out of 201974 words
Chapter 12 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt
, yana ci zee ba kunya tazo ta saka hannu sukaci tare , suka gama ta wanke hannunta ta tashi ko plate d'in shiya dauke ,
Da rana haka suka qara fita cin abinci, haka da daddare, Aslam haka ya wuni da yunwa, don ba abincin kowa yake iya Ciba, a kwaishi da kenkyami, saidai ya sha drinks da cake,
Da daddare ba yanda baiyi ba da zee ta bashi had'in kai taqi, saida ta biye mai suka sha romance kala kala, ta zame jikinta , dole ya hakura ya kwanta, nan kuma tunanin Asmah da kamal ya mai sallama da'ker ya samu bacci ya daukeshi,
Washe gari da asuba bayan ya tada ta da'ker ya tafi masallaci kafin ya dawo har ta idar ta koma ta kwanta , tashinta yayi yace tazo zai fara koya mata karatun addini, qin tashi tayi , saida ya mata Jan ido ta taso tana gungumi,
Karatun suratul fatiha yace tamai, tiryan tiryan tayi , sai dan kuskure kad'an kad'an daya gyara mata, surori ma ta iya falaqi da nas da iklas, ganin ta iya na sallah , yasa yaci gaba da koya mata alwala da farillansa da sunnonin sa, da yake taga ranshi a had'e yasa ta maida hankalinta sosai har tadan fahimta, iya nan suka tsaya , yace gobe zasu tashi a sallah da farillanata, jibi kuma suyi wanka,
A haka suka kwashe sati daya da aure kullum sai sun fita safe rana dare yawan cin abinci, ga tunanin Asmah da kullum yake addabar zuciyarshi, ba abin da yake sonyi kullum sai ganinta, zuwan shi gidan uku baya ganinta taje school,
Yau dai Aslam ya gaji da yawan zuwa cin abinci a restaurant , ya qudiri aniyar yau zee zata fara girki,
Bayan sun idar da karatun su na asuba daya zamema zee matuqar takura, nan ya sanar mata batun girki yi tayi kamar bata jishi ba , dama duk haqurinta ya gama karewa akan shi kiris take jira,
Komawa tayi ta kwanta bayan sun gama karatun ba ita ta farka ba sai sha biyu, lokacin tuni Aslam ya fita ya siyo bread ya had'a tea ya qarya, don ba irin tashin da bai mata ba tana ji ta share,
Warwatsi tayi da kayan data cire a nan tsakar d'akin ta, ta shiga toilet tayi wanka , ta shirya cikin kayanta na gado , qananan kaya,
Falo ta sakko nan ta samu Aslam zaune yana danna system dinsa, baiyi fushi da ita ba, bud'e mata hannayenshi yayi fuskarshi dauke da murmushi zuwa tayi ta shige jikin shi, yace"gimbiyata kin tashi " murmushi tamai , ki tashi kije kiyi breakfast, OK tace
Miqewa tayi taje dining nan ta tarad da kayan tea da sinkin biredi sai kofina duddubawa tayi taga iya su kenan akan dining d'in, dawowa tayi gun Aslam wai bataga abincin akan dining ba , ko suna kitchen ne,
Dagowa yayi yace"baki ga biredi da kayan tea akan dining ba " tace "nagani dama sune abincin" yace "eh, tunda baki girka mana ba ai dole tea zamusha" tace"gsky honey ni bazan ci biredi ba , kasan dai yadda zakayi dani don yunwa nakeji, kokuma kaje ka siyo min abinci, " yace "wlh ba inda zani yau inkin matsu ki shiga kitchen a kwai komai ki girka abinda kike buqata "
Tana zumbura baki ta nufi kitchen d'in , kwai ta fasa zata soya , ta kusa kwashe awa daya ta fito tana hada uban zufa,da kwan ba'ki kirin da shi duk ya qone gashi ya ji uban gishiri, hada tea tayi ta zauna , loma daya tayi ta furzar dashi, dole dai boredin taci tabar kwan a gurin ta wuce ta kwanta abinta ba shara ba wanke wanke,
Aslam saida ya gama aikin da zaiyi a system dinshi ya tashi zai gifta ta kusa da kitchen yaji qauri na tasowa da sauri ya nufi kitchen d'in, frypan d'in data soya kwai ya gani akan hot plate d'in data kunna ta soya kwan,
frypan yayi jajur kamar garwashi, da sauri ya qarasa ya kashe hot plate d'in, ya sauke frypan din, Juyowan da zaiyi ya zame ya fad'i qasa tim, kallon qasan yayi fasassun kwaine kusan uku, ruwan su duk ya zube a qasa shi kuma bai kula ba ya taka ya zame, dama ga tsantsin tiles, kitchen d'in yabi da kallo yayi caca yau d'aya da madam ta fara shiga soya kwai, cikin dan fusata ya nufi dakin ta.
Ganinta yayi kwance tayi dai dai tana charting da friend d'inta tana kwasan dariya bata ma San ya shigo ba, ga d'akin baza baza da kaya ,
Qarasawa yayi yasa hannu ya fisge wayarata, dagowa tayi tana kallonshi, cikin dan fushi yace"haba zainab ki tashi ki danyi share share mana kinga kitchen yanda kika barshi ba kyan gani ga falo tunda kikazo gidan nan baki ta'ba share shi ba duk ko ina yayi qura ,kalli dakin nan pls for god sake, bama a batun toilet, haba da Allah komai sai ance kiyi , wa kike son ya gyara miki ke ko kunya bakiji, kiyi baqi,"
Miqewa tayi daga kwancen data ke, tace"dakata Aslam ban gane me kake nufi wai nice zan dinga wanke wanken kowa? Lallai ma da sake, kalleni sama da qasa banyi kama da yar wanke wanke da shara ba tun wuri inzaka nemo mai aiki ka nemo, danni a gidan mu ko tsinke bana kawar wa, aure na kayi ba baiwar ka bace kaji da kyau, OK sai yanzu na gane dama ka auroni ne dan nazo na dinga maka bauta, to wlh baka isa ba karyarka tasha karya " ran Aslam yayi qololuwar baci a tsawace yace"zainab ni kike gayawa irin wadannan banzayen maganganun," tace "na gaya maka kai waye , duk shiru shirun da kaga ina maka qyale ka kawai nayi amma tunda na fahimci baka da mutunci wlh nima bani da shi, " shammtarsa tayi ta fizge wayarta a hannunshi , ta kwanta taci gaba da dannawa.
Ba qaramin kai zuciya nesa Aslam yayi ba da bai rufeta da duka qafa da qulli ba, fita yayi a dakin yaje falo , kasa zama yayi sai safa da marwa yakeyi, daga karshe tausasa zuciyarshi yayi ya dauki tsintsiya da mopa ya share ko ina na part d'in except dakin zee, yayi mopping , ya feffesa air freshener,
shi kwata kwata baya son qazanta, kuma babu abida yafi tsana kamar yan aiki a rayuwarshi , saboda kenqaminshi ko dakinshi shi da kanshi yake sharewa a gida ya wanke toilet dinshi da kanshi , kuma haka ya tashi gidansu banda driver da mai gadi bai taba ganin wani ko wata da sunan mai aiki ba ,komai kannen shi da iyayen shi keyi a gidan su, dan haka shima baiga dalilin daukar yar aiki a gidan shiba ,
yana gamawa dakin shi ya shiga ya yayi wanka yabar gidan , har Allah Allah yakeyi hutun daya dauka a wajen aiki ya cika ya fara fita yana bar mata gidan,
Direct family hause ya nufa part mami ya fara shiga suka gaisa ta sanar mishi Mallam dinsu Asmah ya amince zai fara zuwa gida sati da lahadi yana koyama zee karatu amma da safe zai dinga zuwa sabanin su zahra da yake zuwa da yamma,
Yana fitowa ya shiga part din ga jiya mama nan suka gaisa tana tambayarshi ina kishiyarta , "wai bazai kawota mu gaisa bane, kodan tasan nafita kyau ne take tsoran zuwa mu gaisa" , dariya yayi yace "wane ke kifi amaryata kyau" tace "ba wani nan inda gaske ne ka kawota mu gwada kyau a gani'dariya ta bashi wai su gwada kyau , aiko ya dara , a nan yadan rage damuwan dake damun shi, yana son hajiya mama, itama tana sonshi sosai cikin jikokinta, daga nan falon alhaji baba yaje suka gaisa kadaran kadahan , don har yanzu ba wani shiri sukeyi ba tun abinda ya faru , na kwanaki,
Daga karshe ya yada zango a part din mummy don yau duk yadda za'ayi ko dare zai kai a gidan sai ya tsaya yaga Asmah , don akwai abinda yake son gaya mata,
A main falo ya samu mummy , nan ya zauna suka gaisa , ta tambayeshi zee yace tana lpy,ta sake tambayar suna dai zaune lpy ba wani matsala ko , nan ma yace lpy qalau, mummy tace masha Allah, taja bakinta tayi shiru, tunda dama bawai sun saba fira bane ,iyakarsu gaisuwa,
Katse shirun yayi da cewa"mummy yaran nan fa su zahra" mummy tace"sunje school,amma inaga suna hanya don sunce yau da wuri zasu dawo, lpy dai ko kake neman su".
"Lafiya qalau"ya amsa ma mummy, can kuma ya tambayi abinci, mummy tace bai qarasa yace to ,ganin zaman shirun yayi yawa, wayar shi ya Ciro ya bud'e data ya hau WhatsApp dan ya debe ma kanshi kewa , message ne suka fara rige rgen shigowa, dan yafi sati rabonshi da hawa WhatsApp, saida suka gama shigowa , kaf ya fara bi daya bayan daya yana dubawa Wanda zaiyi reply yayi, daya gama duba message ya shiga status,
Da status din kamal ya fara cin karo, wani short video ne na hotunan Asmah kala kala, wani tana murmushi wani ta bata rai wani tana dariya , ga sunan dai barkatai , wani kuma ita dasu batool, wani wakar soyayya na hamisu bireka yasa akan video ,a kasa kuma gurin caption yasa emojin luv da arrow a jiki guda uku💘💘💘,
Aslam ji yayi kanshi na juyawa ganin wannan status din na kamal, zuciyarshi yaji ya dauki zafi ,
Girgiza kai ya fara yana kwafah can kuma yayi tsaki,
mummy dai na zaune tana kallonshi, bata ce kala ba amma tana mamakin , meya canza mai mood yanzu yanzu haka
Bata gama tunani ba taji yana cewa "lallai kamal watan cin ubanka ya kusa kamawa wlh " mummy dake gefe tace "subhanallahi Aslam kana da hankali" firgigit ya juyo ya kalli mummy , Ashe zancen zucin da yakeyi ya fito fili,
ta sake cewa"me kamal d'in ya maka kake cewa, watan cin ubansa ya kama, " miqo ma mummy wayar yayi ya kunna mata video yace " mummy kalla , kalla fa abin ya saka a status dinshi , duk qattan duniya fa sai sun gama ganinta ," mummy na gama kallo ta d'ago tana kallon Aslam duk mamakinshi ya gama cikata tace" ikon Allah to kai ina ruwanka don yasa hotan Asmah a status dinshi, meye naka a ciki meye damuwarka a ciki, ka sanima ko soyayya sukeyi, tunda kai ka qita, sai Allah ya musanya mata da kamal yaron kirki , kai kuma ya musanya maka da zainabu ba shike nan , ai wannan ba abinda ya shafeka bane"
Duk da Aslam ya Riga yasan kamal da Asmah , soyayya sukeyi saida kalaman mummy ya dake shi , a fili ya dinga furta "soyayya! soyayya!! Kai ina bazai yuwu ba , yanzu mummy inma soyayyan sukeyi sai ku barsu , bakwa ganin kaman cin amanata akayi kenan yana matsayin qani a gareni ya auri ex wife d'ina"
Mummy da mamakin Aslam ya gama kasheta cikin tsawa tace "kaiii Aslam wani irin maganar banza kake yi haka, to a hir dinka inma Asmah da kamal soyayya sukeyi nice wacce zanfi kowa farin ciki da hakan , kai Allah yasa hakan kaje anci amanar taka kayi abinda zakayi, " kamar zaiyi kuka ya dinga maimaita " haba mummy haba mummy haba mummy" mummy tace"don't call me" ya bud'e zai CE wani Abu Asmah tayi sallama a falon, dukan su juyowa sukayi suna kallonta, ita karan kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin wannan kallon...........
Pls fan's kuyi haquri kwana biyu muna biki ne ,amma mungama jiya, posting will be continue, insha Allah, no stop
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fi sabilillah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar sa wannan book d'in ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 49 & 50
qarasowa tayi cikin falon tace "mummy sannu da gida " murmushi mummy ta sakar mata tace"yawwa daughter har kun dawo" tace"eh mummy"
Kallon Aslam tayi daya qure ta da ido kamar yau ya fara ganinta, ita ta manta da wani Aslam don rabanta da shi tun washe garin auren shi da yazo da safe, "sannu ya Aslam " tace, bata jira amsarsa ba ta haura sama abinta, binta yake da wani irin kallo har ta bace ma ganin sa ,
Mummy na lura da duk wani motsin shi, ta gama harbo jirginshi kaf, akan Asmah, murmushi tayi a zuciyarta tace"yaro man kaza"
Su batool ne suka shigo suna hayaniyar su ,turus sukayi ganin shi a falon su , don rabonsu da shi tun a gurin dinner, gaida shi suka fara yi ya amsa musu kamar yadda ya saba a dake, kamal ne ya shigo shima dauke da jakar Asmah , ganin su a falo ya gaida mummy , miqama Aslam hannu yayi , da'ker ya miqa nashi hannun ganin irin mugun hararan da mummy ke watso mai, ohoo shi kamal bai sanma yana yi ba,
Mummy tace" my son kaima har ka dawo ne haka da wuri yau" yace" a'a mummy nad'an samu free time ne , shine nace bari na dauko qannai na da kaina," mummy tace"kako kyauta wlh" murmushi yayi yace "mummy bari na koma" tace "to kamal Allah ya tsare". rarraba idanu ya shiga yi a falon alamar yana neman Abu , duk mummy na hankalce da shi, ganin dai bata falon yasa ya miqama batool jakar ta , yace"batool ga jakan Asmah ki bata " juyawa yayi ya fice a falon yana qara ma mummy sallama,
Suma su batool d'aki suka wuce bayan sun gaida mummy, mummy ma miqewa tayi ta nufi kitchen, don ta duba abinci ganin yaranta sun dawo, koda ta gama kuma bata dawo falon ba ta wuce d'akin ta.
Aslam ci gaba yayi da zama a falon shi kadai sai saqe-saqe yake, kusan twenty minutes mummy ta dawo ta duba abincin ta yayi ,don haka ta jere a dining,
Falon ta dawo tace ma Aslam abincin yayi ready , cewa yayi yace ,"ya qoshi" daga kafad'a mummy tayi , alamar, ko a jikina d'innana, ta wuce dinning abinta,
Su batool saida sukayi wanka sukayi sallah , sannan suka fito falon donyin lunch, still Aslam na falon,
Yana jin mostin step ana saukowa daga upstairs ya dago kai ya qurawa hanyan ido, kuri idanunshi a kanta baya ko keftawa,
Su basu ma san yanayi ba , dinning suka nufa , anan suka tarad da mummy , serving d'insu mummy tayi suka fara yin lunch d'insu hankali kwance,
Ganin sun manta da wanzuwarshi a falon ne yasa ya miqe ya nufi dining d'in, mummy ta kalle shi tace "ya akayi ne , ko zaka koma kenan " yace " no zanje part dinmu ne wajen amir, kibra Asmah abincin ta kawo min inta gama' to kawai mummy tace, fita yayi daga sashen mummy ya nufi nasu sashen,
Zama yayi a falo yana jiran zuwan Asmah, so yake ya gargad'e ta , ta rabu da kamal taje ta samu mijinta a wani zuri'ar , ba tasu ba, shi daso samune ma ta samu miji acan wani gari inda zai daina ganin ta ko zai samu salama da irin azabtarwar da zuciyarshi ke mai akanta, can kuma wata zuciyar ta gargade shi da cewa kana tunanin zaka iya jure rashin ganinta idan tabar gidan nan, zuwa gidan wani , bama garin minna ba, a fili ya furta" inaaa! zuciyata baza ta lamunta ba," cigaba yayi da cewa "wlh Aslam ka zama ragon maza tunda baza ka iya tursasa zuciyarka akanta ba, don jarumi shine wanda yake iya tursasa zuciyarshi ya hanata abinda take so" tsaki yaja , ya dunqule hannunshi ya naushi iska tare da furta "Ooh shirt"
Amir da shigowan shi falon kenan ya qaraso da sauri hango Aslam da yayi zaune yana naushin iska, yace " lafiya Mallam kazo kana mana naushe naushen iska a d'aki, kaida waye, ko amaryar take ce ta kunno ka " kallon amir yayi yace "nida wad'an nan yan rainin wayon ne kamal da Asmah" Amir a zuciyarshi dariyar qeta yakeyi amma a fili yayi kamar yana taya Aslam jin haushi, cikin yanayin nuna jin haushin su yace "me kuma suka qara yi maka yau" Aslam kunno status din kamal yayi ya miqawa Amir yace "kalla fa"
Amsar wayar amir yayi yana kallon hotunan saida ya gama kallo tsab ya kashe da wata irin dariyar mugunta harda riqe ciki, a jiye wayar yayi ya tashi tsaye, ya fara rawa yana wakar
♪♪♪abin ya mosta♪
♪♪♪yana dukan rai♪
♪♪♪ya bakin ganga♪
♪♪♪soyayya ce ♥
Qara kunnuwa Aslam yayi ji yake kamar ya shaqe Amir d'in, kozaiji sanyi ,
A part d'in mummy kam suna gama cin abincin mummy ta had'a ma Aslam abinci a tire ta miqawa amira tace taje ta kaimai , a ranta tana cewa yaro in kasan wata baka San wata ba ai, Batool tace "mummy Asmah fa yace aba " mummy ta mata daquwa tare da cewa "gidan ku batool, ni kurma me ce kenan, banjiba ko" batool tace "sorry mummy" mummy tace "cikin Amira da Asmah wa ya saba aika " batool tace "Amira" tace "to kin gani may be yazo cewa Amira ne ya manta yace Asmah'"
Amira na sallama a falon Amir ya tsaya da rawar da yakeyi ya nufota da sauri yana cewa" babyna keda kanki, " murmushi tayi , ya amshi tiren hannunta , gaishe shi tayi ya amsa mata cikin kulawa , tace"abincin ya Aslam' ne mummy tace na kawo mishi". "OK to barin miqa mishi, yanzu kije ki huta anjima zanzo muyi hira kinji" cikin dan jin kunya ta amsa mishi da to sannan ta juya ta wuce,
Ajiye abincin a gaban shi Amir yayi yace "bismillah" ji yayi gaba