Header Ads
Showing 42001 words to 45000 words out of 201974 words

Chapter 15 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jun 2024

1714

Ads at the middle of Article

Aslam ba labari, fitowa zee tayi dan ta samawa cikinta abin tabawa, har ta wuce qofar d'akin Aslam , ko me ta tuna kuma ta dawo , tura qofar tayi ta jishi a kulle da key, knocking ta shiga yi shiru ba amsa, daqe kafada tayi alamar , kai ka sani dinnan ,




Kitchen taje still indomie ta qara dafawa, don shi kadai ta iya , zama tayi ta cuccusa abinta tasha lemo da ruwa , ta qara gaba abinta , kamar d'azu,






Da safe sai gurin qarfe goma zee ta farka tayi matuqar mamakin ganin gari ya waye,kenan yau Aslam bai tasheta sallan asuba bane kome,






A bangaren Aslam kam tun jiya da ya shiga d'aki ya kulle , ba abinda yakeyi sai aikin tunani, takura zuciyarshi yayida kwakwalwarshi , da tunani da damuwa,




ga baci ba sha , don da safe bai karya ya tafi office, kuma a office d'in coffee kawai ya sha, hakan yayi sanadin da zazzafan zazzabi ya rife shi ruf,




Kan gari ya waye tuni ya fice a hayyacinsa , sai wuraren goman safe ya samu dan sauqi ya watsa ruwan sanyi, yayi sallah ,first aid box din dake d'akin ya duba ya dauki , maganin zazzabi dana ulcer yasha bayan yad'an sha ruwan tea da cake,




Komawa yayi ya kwanta yaci gaba daga inda ya tsaya jiya, a tunani,




Zee bayan tayi wanka , ta fito falo ganin ba Aslam, yasa tayi tunanin ko ya wuce office ne abinshi, komai bata ji aranta ba , saima cewa da tayi a fili, "kai ka Sani,nidai tunda , baba tsoho ya hanaka, auren wannan yar iskar yarinyar, mai kama da 'kwara, ya gama min komai duniya,".




Ji tayi baza ta iya cin indomie da safe ba don haka , ta koma d'aki ta dauko makullin mota , saida ta isa parking lot d'in taga motar Aslam alamar, yana cikin gidan bai fita ba,






Ficewa tayi abinta daga gidan ko ajikinta, Aslam yana d'akin shi kwance yaji tashin motar zee alamar tabar gidan,


Tsaki ya ja a fili ya gyara kwanciya, yaci gaba da tunanin mafita da yadda zaiyi ya cire soyayyar Asmah a zuciyarshi , kozai samu salama daga irin azalzalan da take mishi ba dare ba rana,






Yau wasai kamal ya farka daga barci duk wani fargaban shi , ya kau ji yake kamar ma andaura auren shi da Asmah an gama, shiya kaisu school , kuma shiya daukosu,




Su zahra sai tsiya sukema Asmah wai dama soyayya takeyi da ya kamal shine ta 'boye musu,






Da misalin qarfe hudu na la'asar uncle nura mijin ya rabi'ah ya faka dalleliyar motar shi a parking lot d'in gidan surukan nasa, fitowa sukayi shida abokin tafiyar nashi, ba kowa bane kuwa face barrister Adam ,




Suna fitowa abban hanifa ya wurgawa brr Adam harara yace" hankalinka ya kwanta yanzu, kasaka ni kawo ziyara gidan surukai ba shi" murmushi brr Adam yayi " sorry bestie na tallafi ruhin abokin ka wlh in bankai kaina ga iyayenta ba yau bazan iya rintsawa ba, ka wala ni da yawa , kaji tausayin mijin maryama, angon fatima zahra to be, insha Allah"






Bello ne ya musu iso zuwa part din daddy , da fara'a daddy ya tarbesu, gaida shi sukayi cikin mutuntawa kamar yadda suka saba,




Bayan sundan taba hira kad'an , abban hanifa ya gabatar da buqatar su , na neman izinin shi game da neman auren zahra,




Daddy yaji dadin wannan lamari, saboda ya dad'e da sanin brr Adam a gurin abban hanifa , yasan mutumin kirkine kamar yadda abban hanifa ya kasance mutumin kirki, don hausawa kance , in kana son sanin halin mutum ka dubi abokin sa,




Take ya tabbatar musu ba'ayi mata miji ba , kuma ya basu izini su naimi soyayyar ta da yardarta.


Nan suka shiga zuba godiya kamar bakinsu zai tsinke, sai da daddy yace ya isa , sallama sukayi da daddy suka fito, da niyar zasu dawo gobe,


Suna fitowa brr ya dubi abban hanifa , yace "yanzu sai mu shiga ko " abban hanifa yace "ina?" Yace
"Ciki mana, muje na ganta , na gaya mata kasan ance da zafi zafi akan daki karfe" harara abban hanifa ya watsa mai yace" to ai sai ka shiga ka sameni a gida " ya fada yana bud'e motar shi ya shiga, shima bar Adam din shiga yayi , suka fice , a hanya yake cewa" to wlh kuwa yau a minna zan kwana, ni da komawa bidda har sai na samu yardar ta da soyyayar ta," abban hanifa tace" in kuma baka samu bafa " baisan sanda yakai hannu ya bame mai baki ba yace" annabin rahama yace fadi alkhairi ko kayi shiru, insha Allah zan samu amincewarta , bakin ka ya sari dutsen faida" abban hanifa yace" to nidai ba ruwana, ka tattara ka koma bidda gobe ka dawo , don kar ka had'a ni da maryama taga kamar da ni aka had'a baki aka mata kishiya , duk da dai nasan komai zan fad'a ba yarda zatayi dani ba , tunda kanwar matata ce, qilama tace ni na had'a ku" dariya brr Adam yayi yace " ohoo dai kai ka sani, ai kunfi kusa, inagama kai zan dauka ma kakai mata kayan fad'an kishiya" abban hanifa yace "rufamin asiri ni bana zuwa irin wad'anan abubuwan , bazan manta ba wani abokina , da ya raka abokin shi kai kayan fad'an kishi ,waishi irin zai mata wa'azi , da makaranta suka tashi ta shaqo shi, saida yayi kwana uku a asibiti ana qara mai ruwa" brr Adam kam mai zaiyi ba dariya ba, cikin dariya yace"kaidai wlh matsora cine abokina",abban hanifa yace"eh naji komai zakace kace, ai mata akan kiyashi zasu iyayin komai , saidai kuma wasu nasu kishin da sauqi akan na wasu," da haka suka qaraso , gida, nan suka qarqare wuni sai dare abban hanifa ya kaishi masauki dan firr qin kwana gidan yayi,






Aslam yauma haka ya kwana cikin mugun ciwo Wanda har yaso yafi na jiya,gaba daya ya fad'a cikin kanqanin lokaci, ya qara haske yayi fiyat dashi, yau abincin ma qin zama yayi a cikin sa , da yasha shayi amai yata kwara wa harda jini jini a cikin aman, gaba d'aya ya gama galabaita, gashi ya saka wayar shi a airplane mood, ba Wanda zai iya kiransa balle asan halin da yake ciki,




Kalaman alhaji baba duk bayan minute amsa kuwwa sukeyi a kunnen shi(ni Muhammad , a mastayina na Wanda aka wakilta ya aurad da Asma'u , na baka aurenta kuma na sanya lokaci nan da wata uku masu zuwa) yanzu shike nan ya rasa husnah kenan , yanzu haka zai zuba ido yana ji yana gani husnah ta auri wani d'a namiji ba shi ba, kai ina hakan bazai taba yuwuwa ba ya zama dole yayi wani Abu akan lamarin nan,


Tunawa yayi da waye alhaji baba , tsayyaye ne kaifi daya, baya magana biyu, take sabon zazzabi ya lullubeshi, wayar shi ya zaro ya kunna hotunan Asmah na rannan yana kallo , da haka ya d'an samu relief,




Zee bata dawo gidan ba sai bayan isha'i don yau garin yawonta ta hadu da wata qawa, wai ita bebalo,bazawara ce, auren ta biyar taqi zama, sai shegen yawo kwararo kwararo lungu lungu, bata nan bata cen, haka suka kulla kàwance, sukayi musayar numbar waya


( dama ance sai hali yazo d'aya ake abota)




Me gadi ne bayan sun gaisa yake tambayar ta Aslam , ganin tun shekaran jiya da ya shigo bai qara ganin fitar shi ba, sai lokacin ta tuna rabonta dashi tun shekaran jiya, tace"kana nufin tunda na fita yana cikin gidan nan bai fita ba?" megadi yace "eh hajiya ,nima naga shirun yayi yawa shiyasa na tambaya ko lfy"
"Ba komai" ta amsa mai , sannan ta nufi cikin gidan zuciyata babu dad'i, duk da tasan akan wannan shegiyar yarinyar ya saka kanshi cikin wannan halin,




D'akin shi ta fara biyawa tayi knocking yafi sau goma , yana jinta amma ya shareta , dan itama yanzu haushinta yakeji gaba d'aya, kowa na duniya haushin su yake ji Asmah kadai yake ji da gani,




Ganin yaqi tankata yasa ta wuce abinta , duk da zuwa yanzu lamarin ya fara bata tsoro,






Washe gari ma haka aka maimaita yaqi bude qofa , ita kuma ganin haka ta shirya ta fita yawanta da sabuwar qawarta beebalo,




Misalin qarfe goma na safe Dr bash yayi parking motar shi a harabar gidan su Aslam , kwana uku kenan
yana neman Aslam ba amo ba lbr har office dinsa yaje amma ance rabonshi da office yau kwana uku daga can ne ya nufa gida dan ya tambaya ko lafiya,




Part d'in samarin gidan ya nufa ba, ba kowa kamal da Amir duka basa nan, kamal na gurin aiki Amir kuma ya fita, ganin haka yasa ya nufi sashen mummy,




A falo yasamu mummy gaisawa sukayi cikin mutunta juna, mummy ta tambayeshi hajiyan shi, da aikin shi duka ya amsa mata da lpy qlau,
Hira suka ta'ba mummy tace"abokin ka dai yayi aure kaima saika fito da taka matar ka aura , tunda dai anyi karatun angama har an kama aiki , Ai kuma sai a godeme Allah a fito da mata ayi aure" cikin dan jin kunya yace "mummy insha Allah muna dubawa , a taya mu da addu'a Allah ya bamu ta gari" mummy tace" amin amin bashir Allah ya baka ta gari" amsawa yayi da amin sannan yace "mummy mutumin nazo nima tun shekaran jiya nake kiran wayar a kashe , naje office kuma aka ce yau kwana uku rabonsa da office shine nazo in duba Allah dai yasa lpy " tabe baki mummy tayi tace"lpy qalau bashir ai lafiya ke buyà inji hausawa" bashir yace "mummy dadai an bincika tunda bawai ya saba yin hakan bane" tace "bashir wannan abokin naka sai a hankali "nan ta labarta wa bashir abinda ke faruwa,




Sai lokacin bashir yasan wacece Asmah daya mace akanta, maganarta yana d'aya daga cikin dalilin da yasa yake neman Aslam ruwa a jallo, jin kuma an bada ta ga kamal harma an saka lokacin biki , a take ya kabbeta daga cikin zuciyarshi, ya dauki dangana da haquri, duk da yasan ba lallai ne ya manta da ita farat d'aya ba,




Bashir yace" mummy a mana afuwa munyi kuskure kar kiyi fishi damu fushinki babban matsalace a garemu, wlh ni karan kaina mummy wata ran nakan rasa gane kàn Aslam , adai cigaba da mana addu'a" mummy tace"ai kudinne bashir kuna kai mutane iyaka, ace kune manya a gida amma qanana ma sun fiku hankali"




Nan dai bashir ya shiga ba mummy hakuri, kafin ya miqe da niyar wucewa ya kuma CE zaije can gidan Aslam d'in ya gani,






Dai dai lokacin motar kamal daya d'akkosu daga school ya paker a harabar gidan , a guje batool ta balle murfin motar ta kwasa da gudu zuwa part din mummy, saboda tsokanan zahra da ta dingayi a hanya , akan wani lecturer daya ce yana sonta ,ita kuma zahra ta tsani mutumin kwata kwata ko zance bataso,shine fa batool ta samu taketa guma mata,ita kuma ta cika tam kamar ta fashe jira kawai takeyi ya kamal yayi parking su yada hali, ita kuma sanin bata da gsky yasa ta kwasa da gudu cikin gida,




Daidai bashir ya sawo kai zai fito itama ta sawo zata shigo, yauma wani karon suka sake maimaitawa kamar dai rannan,


Kowannen su ja da baya yayi , yana Sosa goshi, idanun su ne ya sarqe dana juna , cikin matuqar mamaki har suna hada baki gurin furta , "you again".............






















Oum ummeetarh
07041130088








Share
And
Comment
Fi sabilillah🙏
💖DAMA TA BIYU💖


BY


~AYSHA NALADO ~






FREE BOOK








{ na sadaukar da wannan lillafin ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen












Page 59 & 60










Da kallon mamaki suke bin junan su, lokacin da wancen karon ya faru ya ɗaɗe bai manta fuskar yarinyar ba , tsiwar ta da rashin kunyar ta ya dade yana bashi mamaki,




Itama tayi matuƙar mamakin ganin shi a gidan su , kuma a part din mummy, amma hakan bai hanata ɓalla mai harara ba, cikin tsiwa , tace" wai kai Mallam me kake nema danine, ko wani lokaci muka haɗu sai ka bangaje ni, to wallahi kayi na farko kayi na karshe, duk sanda ka sake bangazata saina sa Allah ya isa" ta qareshe cikin murguɗa baki,








Shi abin ma dariya ya bashi, amma ya dake baiyi ba don kar ta rainashi, don ya lura yarinyar kwata kwata bata da kunya, kara hade rai yayi, cikin dakewa yace"waike me yasa baki da nutsuwa ne, kullun in zanganki kina cikin gudu sai kace wata qaramar yarinya , koda yake yarinyar ce, don da ganin ki ba kifi twelve years ba"




Cikin zaro tace "kan uba, nice Mara nutsuwa"


Kafin ya bata amsa su Asmah da kamal sun karaso wajen


Hannu kamal ya bashi suka gaisa, su Zahra ma suka gaisar da shi , a fakaice yake satan kallon Asmah, a zuciyarshi kuma yana raya "lallai kamal yayi dace, yanzu dama Aslam wannan zuqeqiyar yarinyar aka aura mai ya saki, lallai ya tafka babban kuskura, yayi wasa da damar shi ta farko, gashi kuma bai samu dama ta biyu ba,






Ganin sunzo gurin yasa batool ta hadiye sauran rashin kunyar da tayi niyyar sauke mai , amma fa sai banka mai uban harara takeyi, duk yana lura da ita,




Shigewa ciki yan matan sukayi yayinda Dr bash da kamal suka tsaya suna magana,




Suna shiga batool ko gaida mummy batayi ba tace" mummy dan Allah mutumin daya futa yanzu daga part ɗinnan meye alakar mu dashi ne, ni wlh haushin shi nake ji, ya fiye shegen iyayi wlh"




Mummy zuba mata ido kawai tayi tana kallonta ta inda take shiga bata nan take fita ba sai masifa takeyi , kamar zata ari baki




Suma su zahra duk tsayawa sukayi suna kallonta, saida tayi mai isarta , sannan ta lura da kallon da suke binta dashi,




Kwashewa tayi da dariya mummy tace"sannu mandiya ci gaba mana, ko har kin gama kenen,"


Cikin dariya tace "wlh mummy mutumin bashi da mutunci rannan fa wai marina zaiyi, ranar dinner ya Aslam, har ya daga hannu kome ya tuna naga ya sauke hannun yana kwafa kamar ya Aslam na tafe yana binshi a baya,"




Mummy tace " ai wlh bashir bai biya ni da kakkafta miki mari ba tunda ke kince baki da kunya"




Cikin tura baki ta tashi tana haurawa sama tana dan gungunin, a hankali "tab wlh yana wanka min mari zan rama"


Mummy tace" me kike cewa , ki tsaya kiyi a gabana mana, rasa kunya,"


Su Asmah gaisar da mummy sukayi , sannan suka haura sama dan su kimtsa kafin su fito suyi lunch.






Dr bash yana tuki yana tunanin batool , shi kadai sai murmushi yake yi, can kuma a fili ya furta " kan uba nice mara nutsuwa " cikin kwaikwayan muryanta,murmushi ya kuma saki, kafin a hankali ya furta "ta cika tsiwa" haka kawai ya tsinci kanshi cikin wani irin nishadi na musamman,






Da haka ya iso gidan Aslam , gaisawa sukayi da mai gadi, nan yake shaida mishi matar gidan bata nan amma me gidan yau kwana uku bai saka shi a ido ba, kuma ya tabbata yana cikin gidan bai fita ba , don inda ya fita zai sani ,tunda shi zai bude mishi get,






Cikin mamaki yace ka "tabbatar yana ciki " megadi "yace kwarai yallabai , don ko jiya da hajiya ta dawo ta tabbatar min yana ciki kuma yana lfy"


Dr bash yace " anya kuwa yana lfy, yanzu dai zanje na dauko dan uwan shi Amir zamu shiga mu duba , idan kuma madam ta rigani dawowa ka gaya mata Dr bashir ya zo,"


Megadi ya amsa da to "to yallaɓai a dawo lfy"


Motar shi ya shiga yabar gidan , don zuwa ya dauko Amir,






Karfe biyar daidai na yamma motar brr Adam ta parker a harabar gidan alhaji baba, fitowa yayi daga cikin motar sai zuba kamshi yakeyi, yaci kwalliya cikin dañyar shadda ash colour, sai maiqo takeyi, gsky brr Adam ma ya hadu over,Baki ne dogo kyakkyawan gaske mai siffar dakakkun maza, kallon daya zaka san ma'abocin ibadah ne , saboda yadda fuskar shi ke cike da kamala da haiba, na hasken musulunci,




Megadi ne yamai iso gurin daddy, daddy dama ya riga yasan da zuwanshi don , kuma yasan ba wurin shi yazo ba gurin Zahra ne, don haka ya bada umarnin a kaishi sitting room , a kuma je a gaya wa mummy baƙon zahra yazo




Haka ko akayi mummy dama ta riga tasan za zancen, don jiya daddy ya fada mata komai, itama tayi na'am dashi ganin yadda mijin nata yayi na'am dari bisa dari, tasan bazai yi na'am da abinda zai cutar da ɗiyar wani bama balle ɗiyar shi,




Wayarta ta laluba ta kira zahra, tace ta sameta a falon ta yanzu yanzu,


Zaune suke dama suna karatun alkur'ani da sukeyi duk bayan sallan la'asar, ranar da Mallam ɗinsu bazai zoba dama haka sukeyi su biyama junan su, dogon hijabine har ƙasa a jikinta irin mai dan kwalin nan,




Miƙewa tayi tace ma su Amira tana zuwa ,mummy na kiranta, a falo ta samu mummy, zama tayi a gabanta tace"mummy ganin,"


Kallonta mummy tayi kafin tace"kinyi baƙo, yana sitting room din daddy, dauki ruwa da lemo ki kai mishi , daga nan kuma ki saurari meya kawo shi gareki "


Cikin dan mamaki tace"tace mummy baƙo muka, nifa banba kowa izinin zuwa gidan mu ba, ita a tunanin ta wannan lecturer ne daya dameta a school,"




Mummy tace "to tunda ya riga yazo sai kije ki gani ko" amsawa tayi da to mummy sannan ta fice , kitchen ta fara biyawa ta ɗauki abinda mummy ta umarceta sannan ta nufi hanyar sitting room d'in,


Da sallama ta shiga falon, yana zaune ya ƙurawa ƙofar shigowa ido jira kawai yakeyi yaga

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads