Header Ads
Showing 84001 words to 87000 words out of 201974 words

Chapter 29 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jun 2024

1742

Ads at the middle of Article

ya zabar mai ba Asmah ba idan yayi biyayya a karo na biyu ya karba to idan kuma ya butulce yama kanshi.




Bayan sun gama tattaunawa sun tsaida magana nan Alhaji mallam ya bukaci da suje asibiti tare ya duba Aslam fir yaqi saida suka sake kai ruwa rana ya amince badan yaso ba suka tafi, inda suna zuwa kuma komai yazo musu da sauki, Aslam ya nemi yafiya shi kuma alhaji baba ya nuna yamai wani zabi, bayan su Abba sun dawo gida ya Tara su tare da matayensu ya gaya musu halin da ake ciki, kusan dukkansu sunyi farin ciki da hakan dan a lokacin ba karamin tausayi Aslam yaba kowa ba.




Hakance ta kasance haka aka daura auren Asmah da Aslam, Khadijah da Kamal, bayan daurin auren mallam kamar yadda yayi alkawari shida kanshi ya sanar ma Asmah bayan ya damka mata sadakin ta a hannu..............











Oum ummeetarh
07041130088




Share
And
Comment
Fisabillilah🙏


💖DAMA TA BIYU💖


BY


~AYSHA NALADO~






FREE BOOK










{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
















Page 89 & 90








A nan kan tiles din Aslam ya kwana dukda ma ba wani baccin kirki yayi, tunani ya lula ta yadda akayi aka bashi Asmah, kai shikam koma waye ya mai wannan babban alherin , saiya tsuguna har kasa ya gode mai, inda halima har goyo saiya mai ya zagaye gari dashi, ya kudiri aniyar gobe zaije ya samu Abba ya fayyace mai komai, daga karshe kuma ya koma tunani da tsare tsaren yadda zasu gudanar da rayuwar auren su shida husnar shi , har adadin yayan da zasu haifa tare saida ya tsara su a cikin daren nan, sai gabanin asubah bacci ya kwashe shi cike da mafarkai barkatai, gashi nan shida husna da yaran su.




Kasancewar bai samu bacci da wuri ba yasa bai farka ba sai da gari ya waye garass karfe bakwai na safe.


A zabure ya mike yana salati, ganin haske ya cika falon, anan toilet din falon yayi alwala ,ya dawo ya kabbara sallah, addu'o'i yayi sosai akan Allah ya taimake shi yasa Asmah taso shi itama ko kwatan sonda yake mata ne, bayan ya gama ya mike ya nufi hanyar dakin ta, a hankali yake tafiya har wani dan sanɗa yake yi kamar Wanda yazo sata, cike yake sosai da daukin ganin kyakkyawan fuskarta da ya kwana yana mafarkin shi, saida ya kwashe kusan minti goma tsaye yana tunanin ta yadda zai shiga ɗakin, karshe dai yayi shahada ya murda handle d'in kofar ya tura, saidai kuma gam yaji kofar amalar ta murza key, a hankali har yana wani kashe murya ya fara kwaɗa sallama a bakin kofar yanayi yana dan yin knocking kasa kasa




Jiya da'ker bacci ya kwasheta, saida ta gama shan kukanta, da tunanin kamal dinta, sai ayyanawa take, yanzu kamal nacen tare da Khadijah, ko a wani hali suke oho ko sun daidai oho, kai tasan ma zasu daidaita ne, dan Khadijah ma ba kanwar lasa bace, take taji wani tausayin kanta ya kamata, itafa son kamal daidai da kwayar zarra bai ragu a zuciyar ta ba,




(aikam dai kina ruwa yarinya inzaki kama dahir ki kama, don kamal dai tuni deejah yar gayu tamai formatting heart d'in shi😅)




Duk da rashin bacci da wuri da batayi ba jiya hakan bai hanata tashi da wuri ba don tun, karfe hudu ta tashi, tayi ta idabah har aka kira assalatu ta kabbara sallah, bayan ta idar ma bata kwanta ba, azkar dinta tayi, tare da addu'o'i sosai, ta roki Allah da ya yaye mata son kamal a zuciyar tunda yanzu ta zama mallakin wanin shi, bayan ta gama kuma ta shiga karatun alkur'ani mai girma.


Daidai lokacin kuma Aslam ya shiga yi mata knocking yana sallama, sarai taji shi amma haushin shi da takeji bai bari ta iya koda kallon kofar bane balle takai ga budewa, ganin haka yasa ya shiga magiyan ta bule amma fir taki, dan ko muryarta baici arzikin ji ba balle yaga fuskarta da yake maitan son gani.




Gajiya yayi da magiya ya bar kofar ɗakin jiki a sanyaye, falo ya koma ya zauna yana jiran fitowarta shiru shiru awa daya awa biyu, bata ba labarin ta, tashi yayi ya koma ya sake bugawa, zuwa lokacin kam bacci ta koma bata San ma yanayi ba,jin shirun yayi yawa, yasa ya hakura da knocking, tunani ya shigayi me zataci gashi har ana neman karfe goma na safe, yanke shawaran girka mata breakfast yayi yasan idan ta fito ta samu yayi breakfast zataji dadi, shi kuma fatan shi a yanzu bai wuce yayi abinda zai burgeta ba.




Kitchen ya shiga nan kuma yaja ya tsaya yana tunanin mai zai girka mata, wani irin abinci tafi so, tunawa yayi rannan yaji suna fira da batool kowacce na fadin abincin da tafi so idan bai manta ba da kunnen shi yaji tace masar shinkafa da miyar taushe , gashi shi kuma bai iya masa ba, wayar shi ya dauka ya shiga Google ya dubo yanda ake masa , take yaga abin Ashe ba sauki, don sai anjika shinkar,kuma sai barshi ya tashi wannan duk bata lokaci ne, kar ta fito ta bukaci abincin ya zama bai gama ba, dan haka fasa yin masar yayi , ya duba yanda ake doya da kwai, nan yaga yafi sauki, dan haka ya dauki doya ya fere da kyar duk ya zafzaftare doyan ya gama ya yayyanka, ya kunna gas ya daura, yana dahuwa ya tsiyaye ya fasa kwai ma'ishi ya zuba kayan dandani ya hau suya, ya gama ya dafa mata ruwan shayi mai peppermint ya juye a flask ya kwasa ya jera a dinning, kar kuso kuga Aslam at dat time, ya hada wani uban gumi, bayan ya gama ya koma kitchen din ya wawwanke kayan daya bata, ya share ko'ina ya goge dama ya iya share share dan ko lokacin zee shikeyi idan ya gaji da ganin gidan da datti.




Sai kusan sha daya saura ta farka, toilet ta shiga ta sheka wankanta tayi su brush da sauran uzirorinta ,ta fito gaban mirror ta tsaya tana daure da tawel, kallan kanta tayi taga duk ta dan rarrame,ta kara haske," murmushi ta sakarma kanta tunowa da yan uwanta da tayi, a fili ta furta"Ooh su hajiya batool ko a wani hali ake ciki, nasan dai Dr bash zai sha jaraba, Allah yasa dai kar ya raga mata, dan batool inta samu miji laku laku ba karamin wuya zaisha a hannunta ta ba".


shafe shafenta tayi nasu mayukanta da turarukanta, harda su humra da hajiya addawiyya ta hada musu na magani ,fuskarta kam hoda ta dan shafa sama sama da zizara kwalli, sai dan man lips data dan shafa mai danƙo.




Bude tafkeken wardrobe dinta tayi ta dauki kayan ciki ta saka pant da bra, maida kallon ta tayi wurin manyan kayanta dake nan Jere rerass a cikin wardrobe d'in, wani lace ta zaro kalan dark green da ratsin milk, dinkin Riga da zani ne saidai rigar karamine mai play, ta sanya abinka ga faran fata, kalon ba karamin kyau ya mata ba, abin wuya ta dauka fation ne mai kyau da dan kunnayensa da warwaraye ta sanya, dauri ta kashe mai kyau na yan matan zamani,bayan ta yi fakin din dogon gashinta, sai ta fito da jeler shi ta tsakiyan ɗaurin, nan ta fito dass da ita, amarya sak, dirinta mai kyau ne ko wani irin dinki ta saka kyau yake mata, bata taran dinki ko wanne yi tajeyi skirt, zani ko dogon riga, duk Wanda ta saka karɓar ta yake yi, plate shoes ta saka mai kyau, ta bude kofar ta kamo hanya kitchen danta samawa cikinta abinci.






Bata taba tsammanin samun shi a kitchen ba, amma ga mamakinta tana shiga ta ganshi lokacin ya gama mopping yana wanke hannu a cikin sink motsinta yasa shi saurin juyowa, idanunsu ya sarke da na juna, take fuskar shi wa washe da fara'a yayinda ita kuma tayi kicin kicin da nata, ganin shi a kitchen d'in gaba daya yasa yunwar da takeji ma tuni ya koma, cikin tsananin jin dadin ganin ta yace "gud morning my luv fatan kin tashi lafiya ya bakunta," jin abin tayi wani banbara kwai a zuciyar ta tace, wai my luv, waye my luv d'in, wlh badai ni ba, can dasu gada, a kai kasuwa.




ganin taki amsawa tana mishi wannan kallon nata dake sage mai gwuywa, yasa cikin faɗaɗa fara'arsa yace"kina bukatar, abincin breakfast ne, ai nama riga na girka miki, nasan zakiji dadin girkina sosai muje dining nayi serving dinki kinji baby na" ya karashe maganar yana kokarin riko hannunta, bige hannun shi tayi tare da banka mai harara, kafin taja tsaki ta juya ta bar shi nan tsaye.






Falo ta dawo ta zauna, ganin shi da tayi da safen nan gaba daya taji ranta ya baci, zuciyarta tayi kunci, kwata kwata bata bukatar ganin fuskar shi a halin yanzu, ada tana jin haushin shine saboda irin musguna mata da yayi a baya,ya nuna mata tsantsar tsana da tsantsar kiyayya,
Hakan yasa itama tamai mugun tsana mai tarin yawa, amma a yanzu tanajin haushin shi akan rabata da masoyin ta na gaskiya da yayi, tasani shine ya mata shamaki da auren zabin zuciyarta, wai yana sonta ta ya ya zata yarda da wannan tatsuniyar gizon, Ai ko duk jikin ta kunne ne baza ta taba yarda da hakan ba, karya ce kawai yaudarace, kuma Allah ya fishi ta Allah ba tashi ba.




Shikam tana wucewa ya bita da kallo yana sakin murmushi, ko kadan hakan bai bata mai rai ba saima wani mugun kyau da yaga hararan ya mata, shida zai samu ma ta dinga mai irin wannan hararan ai zama zaiyi ya dinga kallonta kamar TV, da sauri ya biyo bayan ta zama yayi a gefenta, yadan karkato ta yana fuskan tarta, cikin lallashi yace"baby na debo miki abincin na kawo miki nan ne," share shi tayi kamar batasan Allah yayi ruwan mutum a wajen ba, bai daddara ba ya kara cewa "to ko na hada miki tea ne, na dafa miki ruwan shayi mai peppermint, nasan kina sonshi sosai ko" nanma shiru tamai bai damu ba yaci baba da cewa " to in baki son su duka ki faɗa wani abinda kike so saina girka miki," shiru again, mararaice murya yayi yace "don Allah my husnah ki bude bakin ki kimin magana naji muryar ki hankalina ya kwanta,dan Allah, ko zagina ne kiyi, shirun ki a gareni tamkar poising ne".




Gaba daya ya gama takura rayuwarta itafa duk wani Abu daya shafi Aslam bata son shi, a yanzu, maganar nan da yake mata ji take kamar yana diga mata ruwan dalma a zuciya, fahimtar da tayi sonjin muryarta yake kamar hauka, yasa ta kudiri aniyar saidai ya mutu amma ko shekara zaiyi yana mata magana baza ta tanka ba, kai ko zaginta yayi zata iya daure wa dadai ta bari yaji muryan ta da yake maitar son ji.




Zuciyar shi ce ta bashi shawara kan yajeya debo abincin ya biyo ta dashi nan wata kila inta ganshi taci, tsam ya mike ya nufi dinning ya shaqo plate da doya da kwai ya kawo ya ajiye a gabanta ko kallon inda plate d'in doyan yake batayi ba, sake komawa yayi ya hado mata tea ya kowa, ganin tana nan yanda ya barta ko fallon abincin batayi ba yasa ya dauki plate d'in ya zauna daf da ita ya dago doya daya a hannun shi ya kai kusan bakinta yace"haaa my husnah na ciyar dake da hannayena har sai kin koshi," shiru ba amsa, kara matsawa da doyan yayi daf da bakinta har yana dan mannuwa da lips dinta, ranta ne taji ya kara baci,a zafafe ta mika hannunta ta bangaje hannun shi, da karfi , take plate d'in doyan ya kufce ya watse a falon, tashi tayi ta banka mai harara, taja dogon tsaki, ta tsallake shi ta wuce ciki abinta.




Binta yayi da kallo har ta bace ma ganin shi, murmushi ya saki yana girgiza kai, ko kadan baiji haushiba saima wani burge shi da ta kara yi.




A haka suka kwashe kwana uku,ba wani sauyi har zuwa lokacin kuwa Asmah bata taba cema Aslam ci kanka ba, yayi nacin jin muryar ta harya gaji, girki kuwa haka zai mata na safe ya mata na rana da daddre ma ya mata, amma bata taba ɗanɗanawa ba koda wasa, shi kuma bai fasa yi ba, kuma bai taba gani ta shiga kitchen da suna girka wani Abu dan taci, baisan me take ci ba, a ɗan kwana ukun nan idan kuka ga Aslam duk ya sukurkuce ya zama wani iri sai rama yake karawa, dama bai gama maida jikin shi ba, na ciwon da yayi.




Yau kam da suka cika kwana hudu tun safe yake zarya kofar dakin ta yana knocking, tun safe bata fito ba balle ya samu ya ganta, har gashi karfe ukun rana ake nema, gaba daya hankalin shi ya tashi gashi yayi yayi tayi magana taki, ko waya zata yi dasu zahra ko mummy kasa kasa takeyi da murya don kar yaji.




Da gangan taki fitowa yau kwata kwata, abincin kam cincin da cake dasu dublan da soyayyen naman da take dasu a dakin su takeci tasha ruwa abinta, tanajin shi yana ta magiya amma ta share ko kadan bai fara bata tausayi ba, gajiya yayi ya silale anan kofar dakin nata ya zauna ya hade kai da gwuiwa.


Zuciyarta Ce ta bata shawaran cewa , me zai hana kiyi amfani da wannan daman da Allah ya baki akan Aslam ki rama duk cin zali da musgunawan da ya miki a baya, ki bautar dashi ki maida shi abin tausayi, yanda baiji tausayinki ba kema karkiji nashi, take kuwa tayi na'am da wannan shawara na zuciyarta, murmushin keta ta saki a fili ta furta"Aslam ka shiga uku dani, dame zan fara ne" ta tabayi kanta, murmushi ta saki tunawa da tayi da wankin ta data dan tara don tunda tazo gidan bata yi wanki ba, kwasa tayi ta cire kakkauran zanin gadon dake kan gado da bargon shi ta hada da kayanta kusan kala bakwai ta tattaro harda kyar take dauka ta bude kofar, abin tausayi yana zaune ya hada kai da gwuiwa yana gyangyadi, ji yayi kawai an watso mai tulin kaya a kai ba zato ba tsammani, firgigit ya bude ido tare da dago kanshi, saidai ganin ta yasa shi sauke wani ajiyar zuciya, kafin ya shiga sakar mata murmushi, kallon shi tayi a yatsine, kafin ta bude baki cikin yauki da yanga tace"ga kayana nan ka wanke min su kuma yau nake bukatar su ka gane ko" wani dadi ne ya lullubeshi maimakon yaji haushi jin muryar yau yafi komai yimai dadi, take jikin na rawa ya kwashi wankin ya ya shiga toilet din dake falon ya fara wanke wa a washing mashin yanayi yana jin wani nishadi na musamman, yau husnah ta bukaci ya mata wani abin wayyo dadi, shi wlh ko abinda yafi wanki zata saka shi zaiyi, haka ya gama wankin nan yaje ya shanhsanya su a waje ya dawo.






A falo ya sameta cike da dauki yana washe baki ya shiga sanar mata cewa ya gama wankin ya shanya, kallonshi tayi ba yabo ba fallasa tace" ka kyauta ma kanka" iya abinda tace kenan ba godi bare nagode, shiko ko a jikin shi a ganin shi Ai hakan wani ci gaba ya samu tunda gashi tana mai magama kuma ta sakashi aiki, shidai hakan yafi mai alheri akan shirunta a gare shi, zama yayi a gefen ta, ta juyo ta kalle shi tace, "pls ka koma ta cen" ta fada tana nuna mai kujeran nesa da ita sosai, ba musu kuwa ya tashi ya koma, shiru ne yadan ratsa tsakanin su, can ya dubeta yace "abincin ki na kan dining tun dazu na girka ko na kawo miki nan ne," dagowa tayi ta kalle shi cike da yanga da jan aji tace" zubo mi gani ko zan iya ci" tashi yayi jiki na rawa yau tace zataci girkin shi, yaje ya shakaro plate da jellop din shinkawa , yako hadu ko a ido, sai tashin kamshi yakeyi, mika mata yayi , ta nuna mai gabanta tace ajiye a nan , ba musu ya ajiye ya koma wurin zaman shi na dazu, daukar abincin tayi ta kai cokali daya bakin ta, ta fara taunawa abincin yayi dadi ba laifi a matsayin shi na namiji ya girka shi, yayi kokari sosai, amma dan wukakanci furzar dashi tayi tana ɓata fuska, shiko tsuru yayi yana kallonta , cikin bata rai tace"wannan wani irin girki ne haka ba dadi sai uban yaji , kamar girkin mayu, gaskiya ni bazan iya cin wannan abincin ba, ka tashi yanzu ka girka min sakwara da miyan taushe sannan ka min farfesun cow tail dan Allah kayi sauri dan in ka bata lokaci zai iya fita raina na fasa ci" tasowa yayi ya dauke plate din gaban ta yace"dan Allah kiyi hakuri my husnah wlh yajin ne yau ya kufce min amma yanzu zanyi miki abin da kike so ki bani 30 minutes kacal" tace "to yadai fi maka " ta maida kanta kan handset dinta taci gaba da charting dinta.




A daukance ya nufi kitchen din ya shiga fereye doyo.................












Ina team Aslam ku kawo mishi dauki hilis karku barshi ya daka doyan nan😁








Oum ummeetarh
07041130088








Share
And
Comment
Fisabillilah🙏


💖DAMA TA BIYU💖


BY


~AYSHA NALADO~








FREE BOOK










{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
















Page 91 & 92
















Da kallo ta rakashi har ya shige kitchen d'in, sauke ajiyar zuciya tayi, gaskiya yanda taga yana rawan jikin nan sai ya bata tausayi, a ranta ta shiga

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads