Showing 147001 words to 150000 words out of 201974 words
Chapter 50 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt
dinta tare da cewa "shiiiii, abar tuna baya, duk sone ya janyo hakan, tsananin kauna ne ya janyo hakan, a lokacin da zuciya ta ke tsananin so da kaunarki ni kuma Nike kokarin tursasata da cusa mata tsanarki, pls daga yau bani son kina tada maganar baya kinji my husy" gyada mai kai tayi.
Hannu ya mika yana shafa hips dinta da yaga sun baje sosai saboda zaman da tayi a kan cinyar shi yace "husy ban gane ba kwana biyu naga sai kara cika suke yi, su da nan" ya karashe maganar yana daura dayan hannun shi a boobs dinta da dun dazu suke ta tsole mai idanu, kashe mai ido tayi tace "to ai kaima naga ka canja cikin kwana kin nan." Yace "ai ko Rabin canzawar ki banyi ba, anya kuwa banyi ajiya a nan ba kuwa." Ya faɗa yana maida hannun shi dake kan Boob's dinta kan lafaffen cikinta, tace "haba dai tun yanzu." Yace "to me zamu jira, oya tashi muje muyi test mu gani dan ban yarda da wannan kibar da kike mulkawa ba" cike da mamaki tace test "yace kwarai ko test zomuje kiga yadda akeyi" ya faɗa yana mikar da ita tsaye, shima ya mike, ya kama hannunta suka nufi dakin shi, mamaki bai idasa kashe Asmah ba saida taga Aslam ya bude wardrobe dinshi ya zaro p-test guda ɗaya, tsabar mamaki yasa kasa rufe baki tayi, lallai Aslam ba karamin so yake ma haihuwa ba, ba ƙaramin ƴaƴa yake yi ba, har ya siyo p-test daga fara Abu yau sati biyu, to yaushe ma ya siya ya shigo dashi cikin gidan bata da labari.
Muryar shine ya katse mata tunani, "oya muje toilet, ki bani fitsarin." Cike da zaƙuwa ta mika mishi hannu ya jata hannunta zuwa toilet ɗin, itama tana son cikin sosai fatan ta ace bai wuce hasashen Aslam ya zama gaskiya ba, murfin shampo dinta dake jere a toilet din ya cire ya miko mata, amsa tayi ta shiga cikin jacuzzi tayi fitsari ta tari kaɗan a cikin ta miko mai, amsa yayi ya ajiye, tare da bare ledar p-test ɗin ya tsoma cikin fitsarin, dagowa yayi yana kallo, Asmah ma matsowa tayi ta tsaya kusa da shi suka zuba ma abin idanu, zuciyoyin su na luguden bugawa.
Bayan kamar 2 minute ya nuna musu result ɗin, jiki a sanyaye suka kalli juna, kwabe fuska tayi zatayi kuka ya jayowa jikinshi ya rungumeta yana bubbuga bayanta kaɗan kaɗan, a kunne ya raɗa mata "karki damu my husnah, in-sha Allah zan kara himma muma zamu samu ciki kinji." ta gyada mai kai,daga nan kuma ɗaki suka dawo suka buɗe sabon shafin soyayya.
(Hmmmm na lura Aslam da Asmah Kansu kawai suka sani, sun manta da umman little baiwar Allah, nidai kam daga nan Malaysia zanyi na dauko mana rahoto)
~MALAYSIYA~
Tafe take cikin harabar wani babban private hospital da ake matukar ji dashi a kasar ta Malaysia, cike da nutsuwa take tafiyar ta rungume da katon kyakkyawan babynta dan 6 months ɗaya hannun ta kuma rateye da wani babban jakan masu goyo mai kyau na yan gayu, little Aslam ne yau ya tashi da zazzabin hakori shine ta kawo shi asibitin domin suna da kwararun likitan yara, dan bangaren da ake duba yara a cikin asibitin ma dabam yake, ta samu ganin kwarararen baban likitan yara ya duba shi ya bata magunguna, biyawa tayi pharmacy dake cikin asibitin ta siya dukkan magungunan da aka rubuta mashi, sannan ta kamo hanya zuwa inda tayi parking motar ta, bude back sit tayi ta ajiye jakarta dake cike taf saboda magunguna data siya duk ciki ta zuba su, sannan ta dawo gefen mai zaman banza ta daura little boy dinta akan kujeranshi na musamman dake gurin na yara Wanda idan zata yi driving anan take zaunar dashi ta daddaura mishi belt ɗin kujeran, domin Allah yayi ta da rashin jumirin goya yaro, bata ma iya goyo ba ƙarewa, kuma dake abin ba dadata yayi da kasa ba bata maida hankali ta koya ba.
Zaga yawa tayi ta buɗe gefen driver zata shiga kenan daga bayanta taji ance "zaynab abdussalam mai naira."
Juyowa tayi jin wannan kiran haka, tasan ko wanene wannan ya mata farin sani, suna hada ido ta zaro ido, baki na rawa tace.......
Oum Ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabilillah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
*Mg's skincare*
Manyan mata afito a gyara jiki inkin gyara ke kanki zakiji dadi baki fargaban shiga ko Ina always fatarki tazam tana shining kina walwali ba kwarzane ko daya😍amma kiga wata fuska duk kuraje da tabo😖 ko fuska tass amma kafa baki ko gabobin hannu wuluk🫣 wasu Kuma sunburn yabatamasu fuska sister's sannan ynx lokacin sanyine ko kinagyara fata dole saikin Kara dagewa Sabida dakinyi sake jikinki zai lalace😩Kiga Fata na bushewa tana yakwanewa haba dan Allah mufa Mata dagyara akasanmu☺️macen data amsa sunanta tundaga kallo daya ake ganota🤗duk wacce take bukatan kayan gyaranjiki @mg's skincare sun shahara sun zarce tsara indai awannan bangarenne sbd wnn yanayin ma sunkawomuku ingantattun products Wanda zai Dace daku dakuma yanayin da akeciki baruwanki fatarki zatazam 1 in town😍 domun keda kanki zakidinga sha'awar skin dinki ma balle wani yagani🥰kuma kayansu 100% natural/organic
Mai bukata should chat
08062991549,07046881166,07067210195
Call 08064532391
Team glow/clear skin 👩👩👧👦
Page 117
"Dr bala!" Ta faɗa cikin tsananin mamakin ganin shi a gabanta, murmushi yayi sannan ya ƙaraso gabanta, tare da cewa "na'am zaynab" tace " da gaske Kaine a gabana, me kazoyi nan ya mutanen 9ja ina ƙawata beebaloo, nasan tunda na ganka tabbas zan samu koda number ta da na Daɗe ina nema ne" fuskar shi dauke da murmushi yace"duk wadannan tambayoyi haka a Jere zaynab wanne zan fara amsawa." Ita ma murmushin ta mayar mai tare da cewa "kowanne Dr, wlh nayi matukar farin cikin ganin ka, na daɗe ina fatan haɗuwa da mutumin da na sani ɗan Nigeria." Yace nima nayin farin cikin ganin ki "zaynab kodan na nemi tafiyar ki akan abin da na aikata miki nida ƙawarki beebaloo."
Kallon shi take yi cikin rashin fahimtar inda maganganun shi suka dosa, ganin yadda take binshi da kallon ban fahimce ka ba yasa yace "nasan baza ki fahimce ni ba zaynab saidai idan ni da kaina na warware mini komai, zanso ace kinada isasshen lokacin da zaki iya aramin koda minti talatin ne muyi magana." Tace "OK babu komai domin nima inason na nemi wani taimako a wajen ka."
Waiwaigawa yayi yana Neman musu inda ya dace su zauna, can ya hango kujeru guda biyu a bakin wani umbrella tree, cikin inuwa daga gefen su, nuna mata wajen yayi tare da cewa "idan babu damuwa zamu iya zama a cen."
Kallon gurin tayi inuwa ne kuma bugu da kari ba hanya bane babban da mutane zasu dinga wucewa barkatai, "is ok." Kawai tace tare da rufe motar ta, ta zagaya ta buɗe gefen da little boy dinta yake ta dauke shi.
Bayan sun zauna, zee ta ce "Dr na tambayeka ina ƙawata baka ce komai ba nayi missing dinta sosai kullum fata neke Ina addu'a Allah ya haɗa ni da wani dan Nigeria wanda na sani,na aikeshi gareta,ban samu ba sai yau da Allah ya haɗani da kai." Mai makon Dr bala yaba zee amsa sai ya shiga binta da wani irin kallon tausayi, a zuciyar shi ya ayyana lallai mutum abin tsoro yanzu dama haka zaynab ke kaunar beebaloo amma taci amanar ta, ganin yayi shiru yana binta da wani irin kallo yasa da dan karfi tace "Dr bala " firgigit yayi kafin ya sakar mata murmushi, yace "sorry zaynab kinga na tafi wani tunani daban ko,ina mamakin yadda mutanen duniya suka dauki cin amanar masoyin gaskiya Abu mai sauki" kallonta yayi ya fesar da zazzafan huci daga bakinshi sannan ya fuskance ta sosai yace"zaynab na haɗa ki da girman Allah, da darajar da Allah yayi wa ma'aiki ki yafe min." Cike da mamaki tace "Dr bala yafiyar me kake nema a gareni ni baka min laifin komai ba." Yace "na miki zaynab, nine fa nayi sanadin zubewar cikin jikinki, Wanda sanadiyar hakan na fuskanci tarin ɗalu bale yanzu haka maganar da nake miki, an sallameni daga aiki, sannan an kulle min asibiti na mai zaman kanshi, bugu da kari mahaifina jin labarin abin da nake aika tawa na zubar ma da mata ciki a asibiti na , ya kamu da ciwon zuciya take ya yanke jikin ya faɗi, tun daga ranar har yanzu baisan inda kanshi yake ba, da yaɗan bude ido sunana kawai yake kira yana cewa na cuce shi, shi ba irin wannan tarbiyar ya bani ba, yanzu haka likitoci sun hanani zuwa kusa dashi saboda samun lafiya shi, duk wannan abin ya faru ne ta dalilin alluran dana miki.
Nufasawa yayi kafin ya daura da, cewa, "na zubar ma da mata sama da ɗari ciki a duniya amma akan naki naga aya, ban sani ba amma ina kyautata zaton mijin kine yayi binkice ya gane nine na miki allura, shine ya kai sunana ministry of health, aka shiga binkice a kaina har allura ta tono galma, yanzu haka case lin bawai ya mutu bane kotu zamu shiga nan da wata ɗaya, nan kuma da kika ganni mahaifina ne jikin yaki daɗi shine aka turo mu nan, shiyasa dana ganki naji daɗi domin na nemi yafiyar ki,ko Allah zai tausaya min ya rangwanta min."
Tun kan ya gama bata labarin idanunta ya cika da hawayen tausayin shi, girgiza kai tayi cikin tusayawa tace "ash'sha! Gaskiya Abu baiyi daɗi ba, na tausaya maka màtuƙà, kuma ni dai baka min komai ba Dr saboda nina kawo kaina gare ka, Allah kayi wa laifi Dr shi ya kamata ka roƙa ya yafe maka, nima a lokacin jahilci ne yakai ni ga aikata hakan,amma yanzu alhmdllh Allah ya raba ni da wannan mugu ciwo na jahilci duk adalilin abinda ya faru, wannan lamarin daya faru ya zama silar shiryuwa ta,ta farkin Allah madaukakin sarki ya zama sillar tonuwar asirinka a duniya domin ka tuba ga ubangiji kafin ka riskeshi a matabbata, sannan Allah kadai yasan mutane nawa wannan lamarin yayi sanadin fitarsu daga halaka, kamar yadda ya zama silar fitar mu nida kai."
Tunda ta fara magana yake bin ta da kallo, lallai wannan zaynab din tasha bambam da wacce ya sani a watanni baya da suka shude, zaynab ɗin da ke gaban shi wayayya ce mai hankali da nutsuwa mai hangen nesa, ba kamar zaynab din daya sani a baya ba shashasha mara wayau, wacce wata ballagazar mace kamar beebaloo ke Jan ragamar rayuwarta.
Cigaba tayi da cewa " duk wannan faɗi tashi da aka sha bai sa mun iya kashe abinda bamu muke da ikon kashewa ba." Ta karashe maganar tana mika mishi little Aslam dake hannunta, da wani irin mamaki ya ɗago yana kallon yaron da take mika mishi, tace "ka daina tantama ko shakka wannan ɗan da kake gani shine dai Wanda ni da kai da ƙawata muka so hallakawa Allah bai nufa ba." Da wani irin sauri Dr bala ya amshi Aslam a hannunta ya rungume shi a kirgin shi, ya shiga jerowa ubangiji kirari da yabo.
Yana gama wa ya daga yaron sama ya caɓe tare da cewa "hakika kai dan baiwa ne Wanda zuwanshi duniya ke tattare da wani bayyanan nan haske." Ɓangale baki yaro ya fara yi yana dariya kamar yasan abinda Dr bala ke cewa juyowa yayi ya kalli zee yace"ki bani labarin yadda akayi cikin nan ya rayu." Sauke numfashi zee tayi take idanunta suka fara tsiyayar hawaye tuna wa da tayi da abinda ya faru tsakanin ta da Aslam dinta bayan barowar ta Asibiti, saida ta share hawaye sannan a hankalinta shiga labarta wa Dr abinda ya faru tun daga barowarta asibiti, matsanancin ciwon maran da taji jinin da ta zubar dawowar Aslam dukan da ya mata kwanciyar ta a asibiti zuwa kiran mahaifinta da tayi kulle Aslam da yayi da irin dukan daya sha a station, har zuwa fisgarta da mahaifinta yayi daga police station zuwa airport da dawowar ta Malaysia, karbe wayoyinta da yayi zuwa bayyanar cikin ta yunkurin zubar da cikin da iyayenta suka yi, kin amincewar ta har zuwa haihuwar ta, yadda ta koma islamiyya da nasarar da ta samu a komawar da tayi, har zuwa yau da ta haɗu da shi.
Sauke numfashi Dr bala yayi yace "hakika kinga rayuwa kema,amma kinsan duk waɗanda suka jefa ki cikin wannan walagigin rayuwar." Girgiza kai tayi alamar A'a yace "mutum biyu ne, na daya sune iyayenki wadanda suka haifeki, na biyu kuma wacce itace ummul kaba'isin din faruwar komai, wacce kika dauki yarda da soyayyar gaskiya kika daura mata ita kuma taci amanar ki, ba kowa bafe face ƙawar ki beebaloo." Zaro ido waje zee tayi tare da cewa "meye haɗin beebaloo da faruwar wadannan abubuwa." Murmushin takaici Dr bala yayi, kafin kuma ya shiga zaiyane ma zee komai da manufar beebaloo akan zigata da tayi ta zubar da ciki, da kuma kiran Aslam da tayi ta gaya mishi.
Tun kan ya karkare labarin hankalin zee yayi matuƙar tashi, take hawaye suka fara ambaliya a fuskarta, jikin ta ya kara yin sanyi, ta kara yadda Allah abin tsoro ne, duniya abin tsoro ne mutanen cikin tama abin tsoro ne, ta karajin lamarin mutane ya kara fice mata a kai, lallai beebaloo taci amanar yarda taci amanar aminta taci amanar soyayya, da zuciya daya ta riƙe ta, ta dauki ragamar komai na rayuwar ta ta bata duka wani sirri nata ta fallasa mata, bayan Aslam daya kasance miji a gareta a Nigeria beebaloo ce mutum ta biyu da zee ke tsananin kewa da begen gani, lallai ta yarda mutum mugun ice.
Idanunta da suka rine sukayi jajur ta sauke a kan Dr zuciyar ta a dake ta jeho mai tambayar, "dan Allah Dr bala ka fada min gaskiyar abinda ka sani, shin beebaloo tayi nasarar auran min miji bayan barowata 9ja kokuma Allah bai bata nasara ba."
Girgiza kai yayi yace "banajin ta samu narasa akan mijin ki domin kuwa naji daga majiya mai karfi cewa......
~BEEBALOO~
Bayan ta sauke zee a gida ranar da ta kaita asibitin Dr bala aka mata alluran zubar da ciki, da wani irin farin ciki da anushuwa tabar gidan dan ta tabbatar boom ɗin da ta dana zaiyi gagarumar tashi, duk abinda ya faru tsananin zee da Aslam tana da labari komai dan renting ɗin waɗanda zasu dinga bibiyar mata komai tayi na musamman, tun daga kan dukan da Aslam yama zee har zuwa kan barin zee naija tana da labarin komai.
Ranar da zee tabar naije ranar ta fara bibiyar Aslam, ta takura rayuwar shi da kiraye kiraye a waya da message, tun yana dauka har ya gane number ta ya daina dauka, daya gaji ya daga kiran ya mata wankin babban bargo, sannan yayi blocked dinta, hankalinta ba karamin tashi yayi ba hakika tana kaunar Aslam burinta bai wuce a ce yau ta mallake shi a matsayin miji ba, domin ta cika burin ta na auren kyakkyawan namiji mai kuɗi dan babban gida, Wanda kowa yasan wannan dalilin ya hanata zama gidajen aurarrakin ta na baya.
Batayi kasa a gwuiwa ba ta sake siyan wani layin taci gaba da bibiyar Aslam, tana ci gaba da yada manufar ta bata fasa ba, kwatsam ta zo ta daina samun shi kwata kwata a waya duk wani hanyar sadar wa da take bibiyar shi ta yanke, a lokaci guda, (idan Baku manta ba lokacin da ake tsaka da tirka tirkan nan kenan, lokacin da ya kwanta rashin lafiya kafin bikin shi da Asmah).
Hankalin beebaloo yayi matukar tashi fa kasa samun Aslam da tayi kwana biyu, ita fa ta lashi takobin ko ta halin ƙaƙa saita mallaki Aslam, domin wahala da faɗi tashin ta bazai tashi a banza ba, ta shiga damuwa a cikin kwanakin nan taje gidan shi yafi sau a kirga tana samun gidan garƙame da kwado, har ciwo tayi a cikin yan kwanakin nan.
Tana cikin wannan halin Allah ya haɗata da wata tsohuwar kawar ta tun na yarinta, wata rana taje asibiti ganin likita, nan kawar ta mai suna hajo ta tambayeta meke damunta, bata boyema hajo komai ba ta gaya, murmushi hajo tayi tace"kawata kwantar da hankalinki in-sha Allah kakar ki ta yanke saƙa nizan taimaka miki ki mallaki koda uban Aslam ne bama Aslam ba, ki tanadi kudi masu dan kauri ki shirya jibi zan raka ki gurin mallan kamsusi, aikin shi kamar yankan wuƴa yake."cikin tsananin farin ciki beebaloo ta shiga jerowa hajo godiya gida ta koma ta shiga buga buga ta saida wance ta saida wannan ta samu ta haɗa kudin ta masu kauri, bayan kwana biyu suka dauki hanyar gurin malam kamsusi ko sallama da gida beebaloo batayi ba.
Tafiya sukayi sosai a mota kafin su sauka a bakin hanya, suka tari me kabu kabu Wanda zai shigar dasu cikin kauyen, tun a gurin cinikin kudin me kabu kabu beebaloo ta sha jinin jikinta, dan cewa sukayi su bada dubu uku uku, ga mamakin ta gani tayi hajo tace muje "ba tare da wani damuwa ba" ita dai bata tanka ba amma a zuciyar ta tace "dubu uku sai kace mutum zaije kano daga minna" haka ta dai ta hau mashin suka dauki hanya, tun ana tafiya ta marmari har aka gaji, har tafiyar ta koma ta fitar hankali, tuni hantar cikin beebaloo ya fara kaɗawa dan ta sadakar hajo ta siyar da ita, take ta fara jero kalmar shahada tun tanayi a zuciya har ta fara yi a baiya ne, babban tashi hankalinta yadda hanyar kwata kwata bashi da kyau, sai shiga ramuka suke yi suna fita, wani tudun kuwa idan mashin ya hau daga ita har driven