Showing 195001 words to 198000 words out of 201974 words
Chapter 66 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt
yake yi, dan tuni Aslam ya katse kiran ya nufi gurin mota cikin sassarfa yama manta tsaye suke da zee da little sai da yaga sun biyo bayan shi, bai amsa tambayar da zee ke mai na cewa meke faruwa ba sai cewa yayi ta shigo su tafi. A tare suka iso da Daddy, bayan sunyi parking gaisawa suka tsaya yi har kasa zee ta tsuguna ta gaida da daddy a mutumce shima cike da kulawa ya amsa mata tare da kamo hannu little mikewa tayi ta nufi part fin Mummy inda tasan Asmah take, gaisawa sukayi da Aslam bayan tafiyar zee, daddy yace "baka tafi office d'in ba bayàn wannan uwar lattin da kayi, har kullum kai baza ka canza ka daina wasa da aikin ka ba. Wanan inda a wani wajen kake aiki ba gida ba da tuni sun manta sun Dade da korar ka." Yana Sosa keya yace "Ayi hakuri daddy wlh wani labari naji mai kama da almara shine na biyo dan na tabbatar." Daddy yace "Au harda kai takira Ashe , to mu karasa ciki muga zahiri." Falon mummy cike da mutane tuni batool, da Khadijah, sun karaso kowacce da danta yayan sun zama yan samari dan suna neman shekara bibbiyu kenan, ga hajiya mama ga Mami ga Abba ga kamal ga ya Rabi'ah kai falo dai cike da mutane ga kuma makota ga kawayen mummy na kusa, zee na shiga batool ta d'ebe ta ta watsar tare da maida kai gefe har gobe bata kaunar zee duk da kuwa irin yadda zee din ke nuna mata kulawa, Mami ce ta fara mata lale da barka tana ga uwar yan uku ta karaso, itama wurin mamin ta nufa dan a nan taga fuska, a mutumce ta gaggaisa da mutanen falon gaba daya harda su batool daya kamata ace su suka gaishe ta, yadda tayi gaisuwar a mutunce haka suka amsa mata da kulawa suna yi mata barka masu tsokanar ta nayi irin su hajiya mama da Mami, ita dai amsa barkan kawai takeyi ba tare da tasan na menene ba, cikin haka Aslam da daddy sukayi sallama nan kuma aka shiga wani sabon gaisuwar da barka barka ,daddy yace "wai kuna nufin da gaske ne kenan Asma'u ta haihu." Hajiya mama tace "kwarai kuwa d'an nan ga zahiri kana gani, Allah ya amshi addu'a ya kawo wa yarinya abu cikin sauki haka lamarin gwanin dad'i." Daddy yace "Allahu akabar Allah muna gode maka daka amshi addu'an mu, ina dan tselan uwan yake na zuzzuge shi da carbi ladan wahalar min da y'a da yayi duk da dai a karshe an rabu kalau." Mummy tace "d'an tselan uwa ko yan tselan uwa, suna ciki suna baccin gajiya, to an zaunu a ciki wata goma sha d'aya fa." Zaro ido daddy yayi yace "wai kina nufin da gaske ukun ne ba zolayata dama kike yi ba." Yadda yayin ne gaba d'aya ya basu dariya suka shiga darawa. kamal ne ya budo hotonsu da Khadijah ta dauka d'azu da ta shiga ganin su ya mik'a wa daddy, kabbara da kirari daddy ya shiga jerowa ubangiji yana kara gode mai a bisa wannan gagarumin kyauta daya basu, first in history a zuri'ar su, an haifi y'an uku, yana kara kallon su yace "to wai wasu iri ne naga dai wannan mai d'an kumatuttukan nan kamar fanke, kamar macece." Ya fada yana pointing d'aya daga cikin su a jikin screen din faskeken wayar kamal, dariya duk suka saka mummy tace "wato itace amaryar tawa kenan ko? To duka yan mata ne kwantar da hankalin ka, sai ka darje." Aslam kam tunda suka shigo falon yaga an shiga haya baya ya samu ya lallaba yashige dakin Asmah ba tare da kowa ya kula da shi ba, suna kwance daga ita har yaran barci suke yi, tunda ya tura kofar ya hango su, zuciyar shi ta shiga dukan uku uku ji yake kamar a kan iska yake tafiya lokacin da yake karasawa gaban gadon dukewa yayi ya zuba musu ido kamar bai ko keftawa kamar wanda ya warke makanta kokuma wanda bai taba ganin jarirai ba, a fili ya furta "yanzu wadannan duka nawa ne ni Aslam, duka nan mallakina ne." Sai kuma yaji hawaye farin ciki ya ziraro mishi, durkusawa yayi a gurin ya gabatar da sujudulsh- shukur, yana dagowa ya koma gaban yara ya tsura musu idanu yarane kyakkyawan gaske kamar y'ay'an larabawa kama suke yi sak da juna kamar an tsaga kara manya dasu kamar ba yan uku ba, a hankalin ya ringa ba kowacce peck a goshi yana yi mata addu'a yana tofawa, sai da ya gama dasu ya maida kallon shi kan Asmah tana kwance tayi fiyaut da ita, wani irin haiba da annuri yake gani yana fitowa daga fuskar ta, sai ya ga ta wani kara mishi kyau sosai a idanun shi, karasawa yayi daidai saitin face din ta, a hankalin ya shiga saukar da kanshi yana son ya subaci labbanta da yaga sun kari yi mai wani pink kamar ta shafa jambaki, bai kai ga hade bakin nasu ba mummy ta turo kofar ta shigo da sauri ya janye fuskar shi, amma abinka da mara gaskiya ganin yadda yayi wuri wuri yasa ta harbo shi a kallo daya, daure face tayi tace "To bismillah faruwa da iyawa, to tun wuri bari na gaya maka bazan laminci wannan iya shegen ba, idan na dauki na Amir naka kam bazan dauka ba danshi na mishi uzirin ita kadai gareshi kai kuwa fa? Wai da yaushe ma ka tsallakemu a falo ka shigo nan." Ta karashe maganar cikin tsatstsare shi da idanun ta, Sosa keya ya shiga yi yana yan kame kame, tace "maza ka fice min da gani,ka karasa kama Dr iso yazo zai duba su ita da yaran." Dr nasidi ya duba ta sosai ya mata dinki danta samu tear sai da ya tabbatar babu wani sauran matsala sannan ya rubuta mata magunguna, ya duba yaran suma sannan aka fitar dasu aka ba kowa ya dauka cike da farin ciki sai hotona ake musu wasu na daurawa a media masu sakawa a status nayi masu tura a Facebook nayi kai harda su tiktok da Insta sai da kamal ya daura, (yan dama ta biyu fans masu yin tiktok a hya kallo lahiya😂 in kunyi kwa dauko mana mu gani muma.)
Asmah taga gata iya gata a wajen yan uwa da abokan arziki ko ta ina tururuwan zuwa mata barka akeyi harda ma wa'inda ba dangin iya ba na baba irin su AyshaNalado😁 kula kuwa ta kawane bangare samun shi take yi baga mummy da daddy baga Mami da Abba ba kai har su Alhaji baba ba'a bari a baya ba, Ummi kam tun kwana uku da haihuwa ta iso kuma a part mummy ta sauka wannan karon dan karma tayi nisa da yaran, kafin ranar suna ya zagayo ta murmure tayi wani irin fresh ta dawo yar cakwai cakwai da ita asalin Asma'un ta babu wanda zai ce itace ta haifi y'ay'a har uku a cikin ta, zee da Aslam kam kullum sai mummy ta koresu suke tafiya dan in suka zo tun safe sai sukai sha daya a gidan hatta little ba'a barshi a baya ba son yaran yake kamar kamar me da an dauke su zaice a bashi kannen shi idan anki ya saka rigima wata ran sai mummy ta make shi dake ita fire fire ce bata daukar fitsara, sai da daddy yaga abin yayi yawa ya taka ma Aslam birki shine suke wucewa tara, ana gobe suna zahra ta iso ita ma da babyn ta dake gudu ko ina, tana daukan yaran tace "um lallai yara kunzo inda ake neman ku, Asmah da y'ay'an kanta wai aiko zaku sha kula aradu." Ranar suna tun da farar safiya gida ya fara daukar harama. Kowa a k'age yake da yaji sunan da Aslam ya saka wa y'ay'an shi dan an kad'a an raya yaki fad'a duk wanda ya tambaye shi cewa yake sai ranar suna, dan rashin ta ido har Alhaji baba daya tambaye kin fad'a mai yayi. Hatta Asmah bata sani ba daga shi sai zee suka san sunan yaran, aiko abin ya matukar kayatar lokacin da liman ya baiyana sunan yaran, mummy ce da Mami da kuma Ummi, aiko abin yama su mummy dad'i kamar me Aslam yasha ruwan albarka ranar kamar ba gobe. Haka akaci suna aka sid'e abin sai wanda ya gani, suna na gani na fad'a akayi abinci da abin sha enough anyi taron da a tarihin gidan ba'a taba yin taron daya kai wannan cika ba, dan yan dama ta biyu fans ma kawai mun ishi gayya, mu kusan dari hud'u muka zo kuma duk saida mukaci mukayi hani'an mani'an harda masu guzirin na dumame😅. Asmah da yara sun samu kaya bana wasa ba dan saida aka cika store biyu manya manya da kaya bana yaran ba bana uwar yaran ba, kudi kuma cash ta samu yafi miliyan biyar daga abokan Aslam na kusa dana nesa, banda masu transfer wannan kuma Allah kadai yasan adadin su, masha Allah yara kam sunyi goshi harda keya😂 .
Second 2 d last page💃💃💃💃💃💃 luwaiiii
Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Paga 133
🔚🔚🔚🔚💃
Bayan taron suna ya watse baƙi na nesa dana kusa kowa ya koma gida lafiya, a nan family hause Asmah da babies ɗin ta suka ci gaba da zaman jego, basu canza wa yaran wani suna ba da sunan da suke kiran iyayen nasu suke kiran su, wato Mummy, Mami da Ummi. Suna samun kula sosai ta ko wane bangare,kafin arba'in yaran sun murmure sun murtuka wani uban ƙiba dumi dumi dasu gwanin sha'awa idan ka gansu zaka rantse yan 3 month ne, haka itama Asmah tayi wani irin kyau sahihi fatar ta ya ƙara haske da gogewa kamar wata balarabiyar masar idan ka ganta baza ka zata ma tayi aure ba balle har ta haifi ƴaƴa har uku , gyara take samu na musamman daga gurin mummy, abin ba'a cewa komai, tunda jini ya dauke mummy bata tsaya wata wata ba ta shiga gyara parta ciki da bai gyara kuwa bana wasa ba, a cewar ta wai tana da kishiya, dole sai ta tashi tsaye sosai akanta dan bata so ta zama bora a gurin miji, hankalin kwance take jegon ta don yaran kwata kwata basu da rigima madara suke sha basu damu da su sha nono ba, itama bata basu sai taga ya cika yana zuba ko ya fara mata ciwo sannan take basu, ko kuma mummy ta takura mata, Aslam kuwa ya zama abin tausayi kullum kafar shi na gidan ba dare ba rana, duk safiyar duniya sai yazo ya duba su kafin ya tafi aiki, haka ma da yamma idan ya dawo yaje gida ya huta zai sake dawowa tare da little dan shima yaron shegen kulaficin yaran gareshi, sai dare zai tafi,haka zai tasa yaran a gaba ya dauki wannan ya ajiye ya dauki wannan, tsakanin shi da Asmah kuwa sai gani sai hange, gaisuwa kadai ke hadasu, dan mummy ta kasa komai ta tsare idan sunyi doguwar fira to a waya ya kiranta, ba karamin wahaluwa yakeyi da rashin ta ba, duk da ga zee a gefen shi amma baya jin zata iya kashe mishi kishin Asmah, yana maneji sosai da ita yana rage zafi amma fa baya samun yadda yake so ko kaɗan, zee daidai da fruits bata san ta sha da sunan gyara ba, haka nan take kara zube, wai dan ma ana cin me kyau a sha mai kyau kenan da ba'asan ya abin zai kaya ba, kullum cikin lissafin kwanakin dawowar Asmah yake yi, ranar da suka cika kwana talatin da tara a gareshi kamar jajibarin karamar sallah haka yake ji, tuni ya saka an gyara mata part din ta tsab an share ko'ina an kyalkyale sai kamshi da sheki ke tashi, ya ware dakuna biyu ya gyara wa babies, daya an shakare musu shi da kayan wasa da kayan karatu da duk wani tarkace na yara,dayan kuma ya saka musu saitin baby beds da wardrobes har guda uku masu mugun kyau da tsada, ba karamin kudi ya narkar wa yaran nan ba dan harta kayan sawan su sai da ya ciccika musu wardrobes dinsu da shi , washe gari kuwa cike da zumuli ya farkar, tun da sassafe yaje gidan yana sauraren yaji Mummy tace yaje ya dawo ya dauke su shiru bata ce ba har lokacin tafiya aikin shi yayi, jiki a sanyaye ya tafi, ranar daga gurin aiki baije gida ba still nan ya dawo amma har yamma bata ce mai komai ba bai ma ga alamar ana wani shirin tafiyar su ba, haka ya karaci wunin shi a gidan har zuwa dare ba wani alamu, da zai tafi sau biyu yana ma mummy sallama tana cewa a gaida mutanen gida, karshe dai ya gaza hakuri yayi, yaga gara yaje ya tunawa mummy yau ne fa arba'in ɗin koda da wayau ne basai ya fito fili ba, har yakai bakin kofa ya dawo yana sose keya yace "mummy nace ba sai an turo kowa dan gyara ɗakin nata ba nasa duk an share an gyara mata shi tun jiya tunda naga yau ne zasu cika arba'in din." Hararan shi Mummy tayi tace "Waya saka? Da wa kukayi in suka yi kwana arba'in zasu dawo, to bari kaji bazan baka ƴata da kananan yara da basuyi kwari ba har uku, sai sunyi kara kwana biyu zasu dawo zuwa lokacin yaran sun yi kwari sosai." Ji yayi kamar mummy ta kwada mai guduma a kai,tsura mata idanu yayi kamar ranar ya fara ganin ta, harara ta kara watsa mai tace "meye kake kallo na kamar wata sabuwar halitta in kana da magana ne kayi ina jinka." Da sauri ya girgiza kai tare da cewa "ba komai mummy." Tace "to oya a gaida gida." Jiki a sanyaye ya fice, tun daga ranar yake ta zuba ido mummy tace ga ranar da zasu dawo shiru shiru har suna neman kwashe wata biyu, zuwa yayi ya samu Abba ya gaya mai, Asma'u tayi arba'in tun tuni mummy ta hana ta dawowa wai sai yara sunyi kwari, dariya Abba yayi yace "yanzu dai ƙaran mummy ka kawo min kenan ko? Kawai ka fito fili kace mummy ta rike maka mata." Zaro ido yayi tare da cewa "A'a Abba wlh ba haka nake nufi." Cikin dariya Abba yace "ɗan nema bari zan samu daddyn ka da maganar in sha Allah za'asan abin yi." Da taimakon Abba da daddy aka samu mummy da'ker ta bari Asmah ta koma ɗakin ta, ba haka taso ba taso ne sai sunyi wata uku cur sannan su koma, itama Asmah a nata ɓangaren kewan mijin ta take amma ko shi bata taba nunawa ba bare kuma mummy. Saka ranar komawar mummy tayi jibi, Aslam kamar ya taka rawa dan murna sai wani rawan jiki yake yi magana daya biyu Asmah, motsi kaɗan Asmah har sai da zee taji abin ya sosa mata zuciya, a cikin satin babu abinda Asmah take sai kai ziyara gidajen yan uwa, da abokan arziki, har gidan su batool da Khadijah da Amira duk taje, Allah sarki zahra ita kadai ce bata kusa. Ranar da mummy ta saka zasu dawo da sassafe yaje gidan wai yazo daukar su, mummy tace yaje ya dawo sai da daddare kamar yayi kuka, fushi yayi ya tafi yana surutai a zuciyar shi, harda su rantsuwa in suka koma basu ƙara zuwa gidan sai bayan wata biyar. Ko kafin ya dawo da daddare sun gama shirin su tsab shi kadai suke jira, ana isha'e kuwa sai gashi, already ta riga tayi sallama da kowa na gidan su Mami da Abba, hajiya mama Alhaji baba daddy duka ba wanda bata sallama ba, yana zuwa kawai da mummy suka ƙara sallama ya dauki mummy karama ita kuma ta goya Ummi ta dauki Mami a hannu suka tafi, suna isa zee tazo ta tarbe su da murnanr ta suka rungume juna cikin farin ciki gaskiya tayi kewar Asmah abokiyar zama ta gari, duk da kishin da ke dankare a ranta hakan bai hanata nuna mata zallar farin cikin ta da dawowar ta ba. Har part din ta, ta raka ta tana dauke da ummi data sauke daga bayan ta, little sai tsalle yake yi yana murna mummyn shi da ƙannen shi sun dawo, rungume shi tayi itama tana karajin son yaron a ranta duk da ta haifi nata ko kaɗan son da take ma yaron bai ragu a zuciyar ta ba sai ma karuwa da yayi, saboda yadda yake nuna son nata ƴaƴan shima, basu wani zaunar ba zee ta kama hannun little tace su tafi sai da safe yaron harda kuka Asmah tace " ki barshi mana anty zee yaro da ɗakin mummyn shi." Zee tace "ba yau ba anty Asmah sai kin gama cin amarci." Ta karashe zancen cikin zaulaya da ɗan murmushin ta na yake a fuskar ta, da sauri ta sa kai ta fice daga dakin, ko rakiya Aslam bai mata ba dan zumuɗi, Asmah ce tamai singnal da ido alamar yaje ya rakata mana, shima da idon ya mata alamar bazai je ba, hararan shi tayi ta haura sama dan ta watsa ruwa ta na shigewa ya maida kofar falon ya rufe da key alamar ya gama fita kenan, ya kwashe yaran ya kaisu dakin su ya kwantar tunda duk a koshe suke ya shiga jijjigasu ba bata lokaci kuwa suka yi barci, dama haka suke yi idan barci zasuyi a tare sukeyi haka ma kuka da daya yayi abu sai sauran su kama suma. Ta samu dakin ta fes sai kamshi ke tashi