Header Ads
Showing 69001 words to 72000 words out of 201974 words

Chapter 24 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jun 2024

1724

Ads at the middle of Article

idan kaga daya daga cikin su idan ba kamata farin Sani ba bazaka ganeta ba , sun daina fita ko compound din gida saida kwakkwaran dalili, batool kam har yanzu bata saduda ba kullum akazo yi musu wani abin da kuka take amincewa, wani ma saidai a kyale ta idan ta tubure.







A bangaren Alhaji baba kuwa ya Riga ya gama magana da iyayen yarinyar da ya zabar ma Aslam a mastayin zabin shi ta biyu a gare shi, kuma alhamdulillahi sun bayar, da hannun bibbiyu, lokaci kawai ake jira,.








Yau ta kama laraba kuma yaune mother's 's day da za'a gudanar a nan fillin gidan karfe hudu ne zuwa magrib, tunda sassafe yayata ta kaina anti bebi mai design da ummi tayi booking dinta tun ana saura sati uku biki ta sauka a gidan, ita da mukarraban ta , wato yaran aikinta, nan ta shiga zanawa amaren design ma gani na fada, lokacin da tazo yiwa batool, batool nata botsare botsare, ita bata so ganin haka anti bebi ta shiga hada kayanta , to dayake kunsan halin mutuniyar tawa badai saurin fushi ba , saida ummi ta jata gefe ta gaya mata matsalar batool d'in, sannan ta yadda ta lallabata suka gama, suna gamawa saiga Khadijah, wai itama anti bebi zata mata batason na yaran aikinta, aiko dai sisina tace batayi, ita amare kadai akace zata ma design, dayake itama yayan nawa kaifi daya ce inda kukasan Alhaji baba ya yayeta, saida aka dinga saka baki sannan ta dan zizara mata kadan baikai na amaren yawa ba, amma shima ya tsaru ba laifi, wata hajiya ce cikin kawayen mummy tace itama na anti bebi take so, tattara kayan ta tayi ko amsa bata ba hajiyar ba, ummi ne tace "anti bebi ki mata mana ko kadan ne" ta dago rannan a hade kamar zatayi kuka tace "gsky ummi baza ta samu ba, baban mami karfe uku yace na dawo idan na wuce lokacin yace bazai kara barina zuwa design gidan mutane ba, ga Rukayya nan ta iya sosai itama, ta mata,.


Yaran aikinta Rukayya da yaya sukuma suka shiga yiwa sauran mutanen gidan , da bakin da kenan da duk Wanda ke bukata, kasancewar suna da sauri karfe uku sun gama ma kowa, nan aka shiga wanka domin shirin zuwa wajen mother's day, haka dai anti bebi ta bar gidan nan ba tare da tama hajiyan nan design ba saidai sunyi canjin lambar waya saboda wata rana.😅


Tun azahar masu decoration suka fara aikinsu kafin la'asar guri yayi shar ba mai cewa compound din gidan Alhaji baba ne,.



Karfe uku da rabi masu makeup har mutum biyu suka diro gidan suka shiga shirya amare,




Karfe biyar gida ya cika ya timbatsa da manyan hajiyoyi kawayen su ummi Dana mummy da mami, da yake ranar ta uwayen amare ne, aiko sun amsa gayyata ba karya.


Ummi da mummy da mami anko suka sha cikin wani uban sun lace fari kar, mai tsadar gaske Wanda a kalla kudin shi yakai rabin million, banda awarware da yankunnaye da abun wuyan gold da kowaccen su ta zuba wuya da hannu, masha Allah su ummi sun sha kyau iya kyau , kana zuwa gurin ba sai ka tambaya ba zaka gane asalin uwayen amare,.




Lokacin da amare suka fito tsit wurin yayi , wasu kuwa miƙewa tsaye sukayi , zabar kiɗima , sunga haduwa iya haduwa,




Can rumfar dake kusa da na amare na hango yan dama ta biyu fan's , kowaccen su ta kure wanka , ta sako na kasan akwati, an hakince akan kujera ana daddana waya,wasun su kuma na fira kasakasa, suwaibaaliyu Ce ta kalli anty naimcy dake gefenta hakimce tace "yaudai karya zai kare zamuyi ido hudu da Asman data rikirkita mana tunanin Aslam din mu" bata kai aya ba, amare suka fito, kakus Hadiza jafar dake zaune gaba gaba, Sai kallon su mummy takeyi tana jero masha a zuciya, ta fara ganin su zabura yayi ta mike dafe da girji, tana zare ido, ta gidan dan darmay kuwa suman zaune tayi, nikam ina zaune kusa da kawata Fulani gal, muna sirri kasa kasa, dan bamuson kowa yaji mu, Kiy kura dake zaune kusa dani ganin ban ma San wainar da ake toyawa ba yasa ta kai min tsunguli a gefen fuska, zafin tsungulin ya ratsani na dago da niyyar kai mata dundu, dan nidai gaskiya ban bari ta kwana, ganin inda take nuna min yasa tuni zafin tsungulin ya gudu, kawata ma ganin na sake baki da hanci ina kallo yasa itama ta daga kai ta kai idonta inda nake kallo, Oum habeeba wayar dake hannunta tana dannawa ne ya subuce ya fadi ba tare da ta Sani ba, Allah ya somu bai fashe ba, daba na karantawa dama ta biyu yau, Fateema kam wutan kanta ne ya dauke dif, zainab kam da yake ta maka bakin glass irin no respect din nan yasa ban gane halin da take ciki ba, daughter Mr salis kam baki da hanci da kunne duka ta bude tana kallon su dashi, fatima bala gazara , salima abdullahi maman lubna, duk suna zaune, suna ba ido abinci,kai wlh dama ta biyu fan's muna da yawa in nace zanta lissafo sunan ku da daydaya sai mu cinye page dinnan bamu gama ba , masu comment wacce bata ji sunan ta ba ma hade a next page,




Sanye suke cikin wani dankareren lace babban nasu mummy, saidai su nasu black color ne kasancewar su farare sol ga kuma gyaran da fatar su ta dauka, karkuso kuga yanda ya musu kyau , an nada musu goggoro ash colour, takalman kafar su masu tsini suma ash hannayen suna rike da wani dan gudul din pos shima ash ,wuya da hannayensu kuwa gold ne kirar dubai, fuskar su kuwa tasha heavy makeup ko wacce na zuba kamshi, kyau kam kowacce ka kalla, sai kayi tunanin tafi su kyau duka idan kuma ka kalli wata itama haka,.




Wurin da aka tanada dan zaman amare , suka zauna cake dankarere mai hawa biyar na daga gefe, haka aka shiga gudanar da program, cikin wayewar kai , mummy ummi da mami kowacce ta fito ta yi godiya ga Allah ta kum nuna irin farin cikin da take ciki ayau haka wasu daga cikin dangi, dakuma wasu kawayen su mummy,.


Anci mai kyau ansha mai kyau, yan dama ta biyu fan's ranar kakansu ta yanke saka, sai cin kaji ake ana kari, kakus kam tunda ta danki dangwalelen kaza, ta tasa a gaba bata karama kowa magana ba, har aka tashi, garin da tace zata bari ma tuni ta manta da batun,.




Gab da magriba aka tashi a wajen taron,.


Washe garin ma haka akasha kumbo shima a gida akayi, gida ya cika ya tumbaza har fiye da jiya , dan yan dama ta biyu fan's, harda wadanda basu zo jiya ba yau sunzo dan sunce ba'za a barsu a baya ba, kwanda suje su kashe kwarkwatan idanu,.






Ranar juma'a kuma akayi walima, a labour kutigi, karfe hudu zuwa shidda, manyan malamai ne mata, masu ji da ilimin addini Dana zamanj suka bada lecture a wurin waliman nan, gaba daya jikin amaren nan yayi sanyi kalau karma batool taji labari, Asmah da zahra kam harda kukan su shabe shabe da majina,.


Karfe shidda daidai aka tashi, can na hango yan dama ta biyu fan's ana shararowa da kafa zuwa bakin titi, dan dai labour kutigi opposite government hause yake ba kowani lokaci ake samun keke napep ba gashi daga gurin zuwa titi da dan nisa ko rabi basuyi ba aka kira magariba , tuni kafa ya dauke a hanyan, su kakus ido ya raina fata, gashi kowacce tayi lodin sabeniyasa kaya guda dan wasu ma irinsu ta gidan dan darmay so bibbiyu suka karba, ana cikin haka Allah ya turo wani mai hilux,nan muka shiga dagamai hannu , yana tsayawa mukaga Ashe bello ne, haka dai ya taimake mu ya lodo mu a bayan hilux din nan zuwa babban titi, daga nan wasun su masauki suka nufa dan kafa yai tsami,nidai da yake inason na dauko mana rahotan , sa kalle da za'ayi bayan magrib , dole na tari napep zuwa gidan alhaji baba nida Kiy kura da Fateema da Oum habeeba,.






Ana idar da sallah aka shiga sa lalle, hajiya mama da kanta ta saka amare a lallai, zo kuga kuka gun yan matan mummy, inda kukasan an riga an daura aure ne, abin tausayi suna tunanin rabuwa da juna , to ai dole tun yarinta tare ake kwana ake tashi, mummy kam kasa tsayawa tayi a wurin a hankali ta silale ɗakin ta , taje ta sha kukanta na kewan rabuwa da yan matan ta, ummi kan dariya ta dinga musu tana tsokanar su kamar yadda ta saba karshe ma wayarta ta dauka ta shiga ri musu video,.




WASHE GARI



Akace rana bata karya, saidai uwar diya taji kunya, tunda sassafe, gida ya dauki harama baki ta gabas ta yamma ta kudu da arewa, kafin karfe tara gida ya cika makil, da jama'a na masaka tsinke,.




Karfe goma daidai babban masallacin juma'an minna ya cika makil da jama'a, idan kaga mutane zaka dauka sallar idi akeyi motoci kuwa tun daga complex har mobile parking ne , yan sanda ke faman kula da gyara fakin motoci, bosso road ranar kasheta akayi saboda cinkoson jama'a indai zakabi hanyar saidai ka zagaya ta bay pass,. Saida duk wani mai muhimmanci ya hallara sarakuna daga garuruwa mabanbanta, haka manyan malamai daga fadin duniya , ga governor da sauran kusoshin gwamnati,.




Haka aka shiga gabatar da daurin aure bi da bi, har saida aka daura na amare biyar rerasss,akan sadaki mafi karanci da albarka, masha Allah angwaye idan ka gansu bakin nan har kunne, karma amir yaji labari sai daukan selfi yakeyi da friend dinsa, Alhamdulillahi aure ya dauru saidai muyi fatan Allah ya bada zaman lafiya,.




Har zuwa wannan lokacin Aslam na kwance a gadon asibiti, amma har nan labari ya iske shi na daurin auren, shidai har zuciyar baya jin zai so wannan zabin na alhaji baba kamar yadda yake son Asman shi amma zai yi iya kokari shi ya danne son da yake ma Asmah tunda yanzu ta zama mallakin wanin shi zaiyi hakuri da koma wacece aka daura mai aure da ita, kawai don dai yama iyayen shi biyayya, zai ta rokon Allah ya saka mishi son ta a zuciyar shi ya kuma cire mishi son Asmah, tunda ba rabon shi bace, yayi imani ya dauki kaddara zaici gaba da jinyar zuciyar shi , har ta warke daga wannan mummunan ciwo da take dauke dashi na son maso wani , amma a zuciyar shi ya kudiri aniyar ana sallamar shi a asibiti zaibar Nigeria dan bazai iya tsayawa yana ji yana gani wani ya angwance da Asmah bashi ba, bazai iya jura ba, ƙasa mai tsarki zai tafi, yaje yata rokon Allah a gaban dakinshi mai tsarki har sai yaji sanyi a zuciyar shi zai dawo 9ja,.






Acan gida kam yinin biki ake yi cikin girma da arziki ko ina manyan mata ne ta ko'ina sai watayawa akeyi, karfe uku daidai jumai mai kidan kwarya ta dasa a tsakar gida, nan kuma aka shiga caskalewa , dama ta biyu fan's kam an samu abinda ake so tunda suka shiga fili kallo ya kama Kansu, nan suka shiga kwangwajewa, jama'a sai yan gulmace gulmace ake yi kasa kasa , su waye wadannan kuma da suka zake haka sunata rawa, basu suka bar tsakiyar fili ba saida jumai ta nade kayanta,.




Duk wannan shagalin da akeyi Asmah nacen kwance kudundune cikin bargo wani zazzafan zazzabi ne ya lullubeta, tun bayan da aka gama daurin aure alhaji Mallam ya kirata ya damka mata sadakin ta a hannu ya mata nasiha mai ratsa jiki, da kuka shabe shabe ta baro falon Alhaji baba tunda ta fada kan gadonta ta kwanta, zazzafan zazzabi ya lullubeta, gashi Neman duniya tama Khadijah a cikin gidan bata ba labarinta , ko mai kama da ita bata gani ba duk Wanda ta tambaya saidai ace mata bari a kira mata ita, saidai tashi shiru a haka har bayan magrib inda motocin daukar amare suka layu a kofar gidan alhaji baba,..............










DAGA YAU INSHA ALLAH DA RANA KO DA YAMMA ZAN DINGA POSTING🙏 dan allah ruwan comment dan mu samu mu karkare da wuri mu shiga sabon buk
(MIJIN NOVEL, zan aura) daga jin sunan kunsan zai nishaɗan tar daku fiye da dama ta biyu kudai kawai ku bani haɗin kai comment dinku kawai nake bukata, ba sai yan dama ta biyu fans kaɗai ba.






NAGODE SOSAI MASU MIN COMMENT HAR KULLUM DAKU KADAI NAKE TAFIYATA😍














Oum ummeetarh
07041130088










Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖


BY


~AYSHA NALADO~




FREE BOOK










{Nasadaukar da wanna book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
















Page 81 & 82
















Tun daga farkon layin gidan alhaji baba har karshen sa motoci ne laye iya ganin mai hange, wanka amare sukayi mami da kanta ta shirya su shirin barin gida, sai sharar kwalla sukeyi, Asmah kam da yake bata da lafiya wata kanwar mahaifiyar ta da suke uwa daya uba daya , da suka zo biki, ita ta mata wanka ta shirya ta har zuwa lokacin jikin da zafi kau.


Bayan sun idar da sallan magriba, ummi har falon alhaji baba ta musu rakiya, acan suka samu daddy da Abba da sauran yan uwa da abokan arziki, zubewa su kayi a tsakiyar falon kowacce kanta a kasa tana hawaye, alhaji baba ya fara buɗe taro da addu'a, kafin ya daura da nasiha mai ratsa jiki take jikin su ya kara sanyi, bakajin sautin komai a falon bayan amon muryar alhaji baba sai shehsshekan kukan amare, yana gamawa, Alhaji Mallam ya ɗauka daga nan sauran abokanan su kowa saida yasa musu albarka, Daddy da Abba ma sun musu nasiha sosai.




Daga nan wurin hajiya mama aka kaisu, itama ba'a barta a baya ba, haka aka ta bi dasu, suna sallaman dangi, mummy kam ɗakinta ta shige ta ɓame, koda ummi ta tura ƙofar dakinta taji shi a rufe a waya ta kirata wai tana inane amare zasuyi sallama da ita, jin haka dama abinda take dugarma ke nan, sai cewa tayi bata cikin gidan su tafi kawai Allah ya bada sa'a.




Mutane ƴan zakiyar amare tuni kowacce ta samu mota ta kame, ƴan dama ta biyu fans haka suka lodu cikin motoci wasu kan cinyan wasu, wasu ma har a boot, nima allah ne ya soni har zan shiga boot dan ban samu guri ba ,kiy kurs ta yafito ni na zauna a cinyarta, su kakus dai ana boot ido ya raina fata, tare za'ayi tafiyar' ma'ana zasu raka junan su, za'a fara kai batool daga nan akai Asmah, sai Amira, sai kuma a zarce bidda inda za'a kai zahra,. Kowacce motar da aka kawo na musamman domin ta aka nufa don sakata saidai hakan bai yuwu ba , dan zahra da batool kam kankame juna sukeyi , suna wani irin kuka mai ban tausayi ganin haka yasa dole aka saka su a guri ɗaya,.




Gidan batool aka fara zuwa dake nan M,I sauka akayi aka shiga da ita gidan sama ne dankarere Wanda misalta muku shi bata lokaci ne, sabo dal haka ma kayan cikin gidan sababbi ne, ga kuma sabuwar amarya, da sabon ango,Abin zad dadi,.




Bayan dangin Dr bash waɗanda da suke nan dan kar bar amarya sun karbe ta, abincin tarbar amarya mai rai da lafiya aka gabatar musu kasancewar suna sauri yasa suka saka a mota idan an koma gida aci,.




Tashi aka shigayi ana fitowa domin tafiya, nan fa kallo ya koma sama dan amare dai kamkame juna sukayi su hudu suna sharban kuka, da'ker aka samu aka banbare su daga jikin juna,.




Kasancewar basu da wasu kawaye sosai yasa wasu kawayenta sabbi ne ma dan a school ta haɗu da su su biyu suka tsaya da ita zuwa sanda ango zai shigo suma su san nayi a bar ango da amaryarsa,.






Ganin abinda sukayi a gidan zahra yasa lokacin da suka isa gidan Asmah, ba'a bari Amira da zahra sun fito daga mota ba, a nan aka barsu aka shiga aka mata rakiya,.




Itama dankarern gida ne mai girman gaske don yayi Na batool biyu, saidai shi part uku ne a gidan dan haka aka lalubi nata aka sakata, itama sabbin kawayenta ne suka tsaya da ita,.




Haka aka garzaya gidan Amir dake albishir, daga nan kuma waɗanda zasu koma gida suka koma waɗanda zasuyi rakiya zuwa bidda kuma suka dauki hanya, saidai muyi fatan Allah ya kaisu lafiya,.




nikam dai bani cikin yan zuwa bidda dan allah allah nakeyi naje gidan batool naga ya zasu kwashe da dr bash, harna kama hanya na ni kaɗai zan tafi, na dawo cikin sanɗa na yafito ummu muhammad naser, na mata kuskus a kunne, itama saɗaɗowa tayi ta biyo ni, ganin haka yasa ameera dake ankare da duk wani motsin mu yasa ta biyo mu a baya da gudu ba yacce muka iya dole muka tafi da ita.






Bari mu fara da mutuniyar taku😜






~BATOOL~






Bayan wucewar su ummi kukanta taci gaba da rerawa, kawayenta sai tsiya suke mata, ko kulasu batayi ba, wata matashiyar mata ne ta shigo cikin dangin ango waɗanda suka amshi amarya da basu kai ga wucewa ba zama tayi a bakin gadon da batool ke zaune can kurya sai sheshshekan kuka takeyi, kasa kasa, hannayenta ta miƙa ta kamo na batool ta rike cikin nata tana dan murzawa a hankali, jin haka yasa batool ta ɗago kai a hankali ta sauke idanunta akan matar matashiya ce don duka duka baza ta haura talatin ba, tsananin kamar ta da Dr bashir yasa batool ta raya a ranta duk yadda akayi kanwar shi ce,

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads