Showing 174001 words to 177000 words out of 201974 words
Chapter 59 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt
al'ajabi magana fal bakin shi amma ba daman yi, haka ya tafi aiken yana tafe yana sambatu, to abin ne da daure kai, shidai yasan ance ciki ne a jikin ta a ranar da suka kaita asibiti kuma ya ɓare, yanxu kuma ya ganta da yaro mai kama sak da mai gidan.
~Asmah~
Bacci tayi sosai dan sai bayan la'asar ta farka, mummy kam koda akayi azahar bata tashe ta ba, ta barta ne tayi barcin sosai ko zata samu natsuwar zuciya, sai dai tana yi tana leka ta lokaci lokaci, ganin anyi la'asar bata farka ba yasa ta nufi dakin da nufin ta tashe ta, tayi sallolin dake kanta kuma taci abinci. Tana shiga dakin ta tarad da ita a zaune bakin bed ta dafe kanta alamar tashin ta kenan, itama jin motsin an turo kofar yasa ta dago kai mummy ce, kamar yadda dama ta zata, murmushi mummy ta sakar mata, tare da nufar ta ta taba jikin ta don taji koya zazzabin ya sauka, salam kuwa babu alamar zazzabin, alhmdllh ta furta tare da cewa "sannu Asma'u kin tashi ya karfin jikin kuma." Gyada kai kawai tayi alamar da sauki don ji tayi bakin ta ya mata nauyi, mummy tace "to sannu kinji ki daure ki tashi ki lallaɓa kiyi wanka da ruwan dumi zaki ji daɗi sai kizo kiyi sallolin dake kanki kinji." Nan ma sake gyada kai tayi, tana yunkurin tashi, taimaka mata mummy tayi ta mike a hankali ta nufi toilet din wanka tayi da ruwa dumi kamar yadda mummy ta umarce ta, ta kuwa ji daɗin shi sosai, alwala ta dauro ta fito daure da towel, samu tayi mummy ta ajiye mata abaya mai kyau sabo fil da hijab gashi kuma ta shimfida mata pray mat, ko mai bata shafa ba ta saka rigar bayan ta maida kayan ta na ciki data cire tunda bata da wani a gidan, tana cikin sallah mummy ta shigo dauke da tray da kuloli a kai, ajiyewa tayi a gefe, ta zauna tana jiran ta ta idar.
A nutse ta gabatar da sallan ta, bayan ta gama kuwa daga hannun tayi ta shiga kwararo addu'o'i sosai akan lamarin dake tunkaro ta, da kuma rokan allah ya sassauta mata kishi ya bata hakuri da juriyar jure abin da zata fuskan ta a gaba.Tun tana yi a ciki har bata San sanda ta fara yi a bayyane ba, karshe ta fashe da kuka, duk mummy najin ta tana kuma amsawa da amin, a tare suka shafa addu'ar da mummy, tasowa tayi daga kan pray mat din ta iso gaban mummy dake zaune a bakin bed, daura kanta tayi akan cinyar mummy ba tare da tace komai ba, hannu mummy ta daura akan ta, ta shiga shafa mata kai a hankali, sauke ajiyar zuciya ta shiga yi, sun dauki tsawon minti 10 a haka, kafin mummy cikin rarrashi tace "Asma'u ki kwantar da hankalin ki, na fahimci abin da kike tsoro, kar ki saka ma kanki damuwa Aslam yana sonki bazai taba wulakan ta ki ba, idan ma yace zaiyi ninan zan tsaya miki sai inda karfina ya kare, ki kwantar da hankalin ki kinji, in sha Allah kema zaki samu naki ɗan da yardan ubangiji ki cire tsoran komai a ranki kinji." Gyada kai tayi alamar to! Mummy ci gaba tayi da kwantar mata da hankali tana gaya mata maganganun masu sanyi ma zuciya natsuwa. Daga yadda ta nutsu tayi shiru ta daina sauke ajiyar zuciyar da take yi mummy ta fahimci zancen ta na shiga ta sosai, hakan yasa cikin dabara ta shiga kowar da ita dabaru zama da mutanen cikin hikima yadda baza ta cuci kowa ba kuna baza a cuce ta. Kwarai ta samu nutsuwar zuciya sosai daga kalaman mummy, ta samu karfin gwuiwar da ta rasa a ɗazu, zafin da zuciyar ta ke mata da ragu sosai daga kashi talatin cikin dari. A baki mummy ta bata abinci don tasan idan tace ta ci ba ci zata yi ba, duk da haka bata wani ci ba. Bayan sun gama still mummy bata gaji ba ci gaba tayi da koya mata wasu abubuwan da zasu taimake ta a zamantakewar ta na yau da kullum.
A massallacin kofar gidan yayi sallan isha'i, ana kuwa idar wa bai ba bata lokaci ba ya shigo cikin gidan a kagare yake daya sanya ta a idanun shi, ya damu matuka da son sanin halin da take ciki, haka kawai zuciyar shi ke bashi tana cen tana kuka, duk da yasan mummy baza ta bar ta tata kuka ba.
Koda ya shigo falon mummy ba kowa sai TV dake ta zuba shi kadai, kasa hakuri yayi ya nufi dakin mummy dan yana da tabbacin tana can, da sallama ya tura kofar dakin ya shiga, tana zaune a bakin bed tayi tagumi bata san ma ya shigo ba, ita kadai ce a dakin mummy ta fito ta dauko mata sako, wanda bata San sakon menene ba. Ganin ta a halin tunani yasa da sauri ya karasa gaban ta duƙawa yayi a hankali ya saka hannun shi ya sauke mata tagumin data yi, zuba mishi idanunta tayi da suke nan a ƙorɗe babu kalli ko ɗis gashi sun kumbura sunyi luhu luhu, kallo daya mutum zai san taci kuka yau taba uku lada. Shima idanun nashi ya zuba mata yana kallon ta, take yaji zuciyar shi tayi kunci take yaji wani haushin zee ya kara turnike shi, duk ita ce musabbabin wannan fitinar yana zaman zaman shi ta zo ta jagula mai lissafi, shi wlh da ace shi ta tunkara kai tsaye da amshe ɗanshi zaiyi ya miƙawa husnah kuma bazai taba barin ta ta isa wajen iyayen shi ba balle har su tursasa mishi zama da ita. Cike da tausayawa yace "husnah kuka ko?" Rintse idanun ta tayi saiga wasu sabbabin hawaye sun ziraro, kafin yakai ga kara cewa wani abu mummy tayi sallama, hakan yasa da sauri ya sake mata hannu tare da amsa sallaman mummy,batayi wani mamakin ganin shi a dakin ba domin dama tana tafe tana tunanin kila ya ƙaraso domin kuwa ita tace mai bayan isha'e. Guri ta samu ta zaune take ya shiga gaishe ta amsawa tayi adan sake ba kamar ɗazu ba, duk da dai ba wai ta sake gaba daya bane. Gyara zama tayi tare da cewa "Aslam! Aslam! Aslam!." Ya amsa da "na'am mummy." Tace "sau nawa na kira ka." Yace "sau uku." Tace "dakyau, ga Asma'u na nan zan damka mika ita a hannun ka a yau, koda gigin wasa kada ka kuskaura kace zaka canja mata ko zaka wulakan tamin ita saboda dawowar matar ka uwar ɗanka, nasani ne ku maza kuna da wuyar sha'ani kuma Baku da tabbas shi yasa tun farko nake buga maka warning karka kuskura kar naji kar na gani, domin wallahi! wallahi! wallahi! A wannan karon bazan laminci ka tozar ta min ɗiya akan wata matar ka ba." Cikin tashin hankalin yace "Mummy dan Allah ki dena fadar irin waɗannan kalaman, tsoro suke bani." Daga hannu yayi sama yace "ya Allah kada ka nuna min ranar da zan juyawa husnah ta baya, idan kuma ka kaddara hakan zai faru a rayuwa ta ya Allah na roke ka, ka dauki raina kafin lokacin." Tuna Asmah ta shiga girgiza kai tana hawaye jin abida yake cewa wai Allah ya dauki ranshi, to ita kuwa meye makomar nata ran idan babu nashi ran, domin Aslam shine ran nata ran. Ita kanta mummy sun bala'in bata tausayi har saida ta dauke kwallah a kafaice, ta kima kara tabbatar wa ba karamin so Aslam yake ma Asmah itama Kuma ba karamin so take mishi ba, shiyasa ta ke tsananin kishin shi. Lallai zee ta shiga hakkin su, amma kuma baza suyi jayayya da ikon Allah ba domin Allah kadai yasan abin da yasa ya turo ta cikin su a daidai wannan lokacin ita dai adduar ta shine Allah yasa zuwanta cikin su yazame musu alkhairin duniya da lahira. tana da tabbacin yadda suke son junan su soai haka mawuyacin abu ne aslm ya juya mata baya sai fai idan sun haɗu da shu umancin mace domin dai tasan wasu matan shu,umai ne Kasa ci gaba da faɗin abin da tayi niyyar faɗawa Aslam ɗin tayi, domin idan tace zata yi magana zata iya fashe wa da kuka, mikewa tayi ta mikar da Asmah tsaye ganin haka yasa shima ya mike, mika mata wani babban leda tayi tace "in kinje ki duba na miki bayanin komai a ciki, kuje, ki bishi kuje gida Allah ubangiji ya muku albarka, Allah Kuma ya cika muku burin ku ya baku ƴaƴa masu albarka." Rungume mummy tayi ta fashe da kuka, shi kam Aslam gaba yayi ya bar ɗakin ya dawo falo, domin sauraren kukan ta zai iya saka shi shima ya fashe da kukan a yadda yake jin kukan ta na taba zuciyar shi. Dakyar mummy ta samu ta raba ta da jikin ta, ta kamo hannunta ta zuwa falo tana zuwa ta kama hannun Aslam ta saka mishi hannun ta a ciki tace "kuje Allah ya baku sa'a." Da sauri ta juya ta haye upstairs. Jawo ta yayi ya tallabe ta a jikin shi ta gefe, a haka suka iso parking lot ya buɗe motar shi ya sanya ta a gefen mai zaman banza shima ya zagaya ya shiga gefen direba, ya bar gidan yaso ya kaita tayi sallama dasu Mami da Kuma Alhaji baba da hajiya mama, to yadda yaga yanayin ta yasan hakan bazai yuwu ba, har suka iso gida babu wanda yace ma wani kala a cikin su, zuwa lokacin ta daina kukan sai shehsheka da ajiyar zuciya take sauke wa akai akai. Lokacin da motar su tayi parking a compound ɗin gidan su daga shi har ita idanun su akan part din zee ya sauka, ganin wuta a kunne ko ina ya dauki haske hakan ne ya tabbatar musu da cewa daddy ya cika aikin shi wato ya kawo zee gidan ta a matsayin matar Aslam a karo na biyu kamar yadda ya faɗa......
Allah sarki Mr and Mrs Aslam sabuwar rayuwa muna muku fatan alkhairi nida mutane yana dana ta biyu fans
Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 127
Shi ne ya fara yin karfin halin buɗe murfin motar ya fito, ya zagayo ta gefen da take ya buɗe mata ita ma, cikin matuƙar sanyi jiki ta fito, mayar da ƙofar motar yayi ya rufe, tare da kama hannun ta suka nufi nata part ɗin.
A hankali ta saki labulen windon data dan ɗage kaɗan tana kallon su, da baya da baya ta ringa ja har ta isa bakin bed ta zauna dabass, tagumi ta rafka da hannu bibbiyu tayi shiru tana jin zuciyar ta na mata wani irin zafi ga wani ƙululun abu daya tokare mata kirji shi bai sauka ba shi bai hau ba,ba sai ta ba kwakwalwar ta wahala gurin gano ko menene wannan ba, ko bata tambaya ba tasan menene, kishi ne, kishin shi take yi matuƙa gaya, kishi kuwa bana wasa ba, amma ta ɗaukar ma kanta alkawari zata jure zata danne, kodan ta dawo da martabar kanta a idanun shi, domin a yanzu tasan da ita da kashi duk daya suke a wajen shi, take hawaye suka balle mata kamar an buɗe fomfo, little na ganin tana kuka yazo ya rungume ta kamar yadda yaga tana yi mishi idan yana kuka ya shiga rarrashin ta yana cewa "Mummah kiyi shiru ki dena kuka zan siya miki sweet mai tsinke da ice cream." Samun kanta tayi da sakin murmushi jin abin da yake cewa, yaron yana da matukar wayo ga uwa uba surutu duk da ba ko wsni lokaci yake magana ba, idan yayi wani maganar takan yi matuƙar mamaki, sau da yawa takan ce, my boy a ina ka kwaso surutu haka, me sunan ka dai shiru shiru ne. Share wahayen ta tayi tace "OK my boy nayi shiru kaji, oya zo ka kwanta haka dare yayi." Kai ya gyada kawai ɗaukar shi tayi suka haye kan bed ɗin suka kwanta, addu'ar bacci ta shiga karanta mishi yana amsawa kamar yadda take mishi kullum, bayan sun gama ya shiga rero mata surutu, shiru tayi ta rufe idanun ta kamar ta yi barci ganin haka yasa shima yayi shiru take kuwa barci ya kwashe shi. Jin alamar yayi barci yasa ta mike a hankali ta zare jikin ta cikin nashi, bata jin bacci kwata kwata, dan ji tayi idanun ta sun bushe ƙamass Ta dawo gidan Aslam burin ta ya cika kamar yadda take so, sai dai Kuma hankalin ta ya kasa kwanciya kamar yadda ta zata, ta dauka idan yau ta ganta a cikin gidan Aslam a matsayin matar sa a karo na biyu shike nan duk wani damuwar ta ya yaye a she abin ba daga nan take ba, a lokacin da ta ta babbatar Aslam ya auri Asmah bayan bata, bata damu ba domin a wannan lokacin bata wannan take yi ba burin ta kawai Aslam ya amshe ta a karo na biyu, amma yanzu bayan ta samu wannan daman sai wani irin masifaffen kishin Asmah ya turnike ta, sai dai ta daukar wa kanta alkawarin zata yi yaki da zuciyar ta baza ta bari ta saka ta ta aikata aikin dana sani kamar yadda ta sakata ta aika ta a baya, toilet ta nufa dauro alwala tayi tazo ta gabatar da sallan nafila raka'a hudu, bayan ta gama ta dauki kur'ani ta shiga karatu, sosai tayi karatun ta, bayan ta idar kuma ɗaga hannu tayi sama ta shiga kwararo addu'a, duk dai akan Allah yasa Aslam ya yafe mata, Allah kuma ya bata karfin halin jure duk wani abu da zai mata, ya kuma rage mata kishin Asmah a ranta. Ba ita ta tashi ba sai kusan karfe ɗayan dare, koda ta hau gado ta kwanta gaban ta ne ya yanke ya faɗi tuno shin a wani hali iyayen ta ke ciki a yanzu, ta sani dole zasu shiga matsanancin tashin hankali musamman Dad, daga kwancen da take ta shiga yi musu addu'a akan Allah ya basu hakuri da juriyar daukar wannan lamari. Ba ita ta samu barci ba sai kusan karfe ukun dare.
A bangaren Aslam da Asmah kam yau suma haka suka kwana, kadaran kadahan, duk da Aslam yayi iya yin shi dan ganin ta saki ranta amma abin ya gagara, ya mata uziri yana ta binta yadda taso, har zuwa safiya bata cikin walwala, ganin yadda duk yabi ya damu sai wani lallaɓa ta yake yi, yasa taji ya bata tausayi dole ta aro walwalan karya ta yafa wa kanta, idan yayi wani abin dan ya saka ta dariya tayi murmushin yaƙe, hakan kuwa ya mai daɗi ganini haka ya samu karfin halin fita office duk da bai daɗe ba sha biyu ya dawo.
A haka suka kwashe kwana uku, zuwa lokacin Asmah ta sake sosai ganin ko kaɗan Aslam bai canza mata ba sai ma wani ƙarin kulawa da tattali na musamman da yake nuna mata, tuni ta ajiye batun wani kishi da wata zee suka bude sabon shafin soyayya, kuma har tsawon wannan kwanakin daga ita har Aslam din babu wanda ya saka zee da little a idanun shi, Asmah tana sane da hakan don lokaci lokaci sukan faɗo mata a rai, sai dai tana tsoron ta saka musu baki dan tana gani wannan tsakanin su ne matsalar su ce su ta shafa, kullum Aslam na part ɗinta bai taba cewa zaije wajen su ba, yadda ma yake yi kamar ya manta da wasu halitta a gidan, itama bata ce yaje ba, sai dai fa a can ƙasan zuciyoyin su tunani da kewar little ya hana su sakat, so ɗaya ta taɓa saka yaron a idanun ta amma ya kama zuciyar ta fiyye da yadda bata yi zato ba, shima Aslam ɗin haka kullum da tunanin yaron yake kwana yake wuni sai dai yaki zuwa gareshi saboda wani dalili da shi kadai ya bar wa kan shi sani, amma fa daure wa kawai yake yi. A bangaren zee kam duk fitar shi da shigar shi akan idanun ta, takan kwana kuka kamar hawayen ta zasu kare, little yayi ta rarrashin ta idan taki yin shiru shima sai ya fashe da kuka, daga karshe ta yanke shawaran da take ganin shine zai ɓullar da ita kan hanya, zatayi amfani da nata kalar hikimar ta karkato da hankalin mijin ta gare ta, bada tsiya koda tashin hankali ba, domin idan wannan tace zata yi a halin yanzu ita ce baza taci riba ba, dan ta riga ta sadakar Asmah ta sha gaban ta, ta ko wanne fanni.
Yau da ta kama kwana biyar da dawowar ta gidan komai na ɗan kayan abincin da ta aiki megadi ya siyo mata sun kare hakan ya saka bayan tayi wanka sun karya ita da little ta laɓe a abakin window kamar yadda ta saba, tana kallo har Aslam ya bar gidan, yana fita kuwa ta zaro galenta ta riko hannun ɗanta suka fito so take ta sake aikar megadi ya kara siyo mata kayan abinci. Daidai sunzo kofar part din Asmah, ita kuma ta buɗe kafar ta fito hannun ta dauke da kwandon shara da alama shiya fito da ita dan ta juye a babban drum dake waje, turuss suka ja birki dukan su suna bin juna da kallo, zee ce tace ta kawar da kallon ta hanyar sakar mata wani irin kyakkyawan murmushi, tana ƙarasowa wajen ta tace "manya idanun ku kenan, kun shige ciki shiru ba ajin ko motsin ku, to yau dai gashi mun haɗu ina kwana ya gajiya ya