Showing 1 words to 3000 words out of 201974 words
Chapter 1 - DAMA TA BIYU completet A'isha Nalado .txt
DAMA TA BIYU
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
Page 1&2
Bismillahirramanirrahim
Wasu k'wawawan motocine masu rai da lpy ke tafiya akan shimfidedden kwaltan dake unguwar London road dake garin minna,
Duk Wanda yasan unguwan London road. Yasan unguwace ta manyan mutane .musamman manyan yan kasuwa,
Kofar wani katafaren gida motocin nan sukayi parking gidane mai kyau. kuma ga dukkan alamu sabon gini ne ba a kai ga tarewa cikin saba,
Ahankali marafen motocin suka fara budewa. Mataye ne suka fara fitowa daga cikin motocin nan.
Yawancin matayen sanye suke da ankon wani hadadden atamfa yellow and brown colour. wasunsu kuma sanye da shiga ta alfarma,
Saida suka gama fitowa kaf d'insu na lura da wata mota guda daya daga cikin motocin nan wadda ba a bude ba balle a kai ga fitowa daga cikinta,
duka matayen nan tsayawa sukayi suna kallon motar nan. da alama jira sukeyi na cikin motar su fito ,
Marfin motar ne ya bude. A hankali wata dattijuwar mata da akalla zatakai shekara hamsin da haihuwa ta fito a motar cikin shiga ta alfarma. Sai kuma wata ta bude gaban motar ta fito ita muka sanye take da ankon dake jikinyawan cin matayen,
Hannu yar dattijuwar data fara fitowa a motar ta miqa ta kamo hannu waccce ta rage a cikin motar.wacce nake tsammanin duka matayen nan ita suke zaman jiran fitowarta ,
A hankali ta sako fararen qafafunta waje Wanda yasha wani irin design na black and red henna.
dai dai lokacin wasu daga cikin matayen nan suka saki bud'a ji kake "ayyiririririyyyyyy" wuri ya haustine da bud'a gwanin birgewa,
Sai alokaci na fahimci meke faruwa a wurin wato dai amaryace aka kawo sabon gidan nan
A hankali na qare ware idanuna akan amaryan sanye take da wani ubansun lace maroon colour mai duhu Wanda yayi masifar yima farar fatarta kyau an lilla'be mata kanta da wani babban mayafi peach colour kafarta da yasha design sanye da takalmi mai tsini shima peach dukda banga fuskar ta ba nasan wannan amaryar masha zatayi kyau ba qarya,
Matan nan biyu da suka fito mota daya da itane suka sanya ta a tsakiya suna nufar gidan sannan sauran matan suka rufa musu baya.
Dai dai get suka tsaya wannan dattijuwar matar tana karanta mata wani addua tana amsawa cikin sanyin muryarta daya shaqe tsabar kukan da tasha,
Da bismilllah ta sanya qafarta cikin gidan . wasu matane suka taso cike da fara,a suka tarbesu har cikin babban plat din dake farkon gidan
Masha Allah ginin bene ne babba Wanda ya gama tsaruwa kamar a Turai an qawatashi da kayan more Rayuwa na alfarma , saida suka sadata da bed room dinta dake upstair sannan suka firfito wasu suka zauna a falonta na sama wasu kuma suka sauqo kasa.. Nan aka gabatar musu da abincin tarbar amarya mai rai da lafiya kowa yaci abinda ranshi keso ya qoshi . nan dai wasu suka zazzaga gidan .. Gidan kam ya hadu sai sambarka
Amarya kam tunda suka sadata da bed room dinta suka zaunar da ita a gefen bed dinta kanta me duqe lilli'be da mayafinta . kuka takeyi sosai kamar ranta zai fits sai shesheqa takeyi kamar zata shiqe. Ita kadai tasan abinda me damun zuciyarta game da wannan qadddararren auren ..dasun San halin da take ciki game da wannan auren da dukkansu sun tayata kukan baqin ciki,
Dama ace zata iya bijirema Alhj baba akan wannan auren hadin daya hada data bijire mai,
Saidai kuma kash ko giyar wake tasha bazata taba iya bijire masa ba , saidai mijin da aka aura matan ya kasheta kamar yadda yay ikirarin cewa. tayarda ya kashetan akan ta zama butulu gurin bijirna umarnin alhj baba..
Tunaninta ne ya katse jin motsin mutane suna nufowa dakin da take domin yi mata sallama .
shigowa suka dingayi suna mata sallama da fatan alkhairi wasunsu na mata addua da tayata farin ciki yayinda wasu zuciyarsu kamar tayi bindiga ta fashe don tsananin baqin ciki .
Wani kukane ya
kufce mata ganin da gaske tafiya za suyi su barta a cikin wannan baqin gidan da ta tabbata shine ajalinta,
Rarrashinta suka shiga yi da bata baki yayi da masu Jin haushinta musamman yan matan dake son auren mijin nata dakuma wadanda kema yayansu ko kannensu kwadayin auren wtakeyiba
ya'kyawan santalelen matashin saurayin mai ji da kudi ga kyau ga 'kuruciya, ke mata kallon wawiya wacce batasan abinda takeyiba
Shere and comment
Fisabilillah🙏🏻
💖DAMA TA BIYU💖
BY
{AYSHA NALADO}
FREE BOOK
Page 3 & 4
Wata mataCikin yan kawo amarya ta karasa kusa da amaryan ta tsuguna a gabanta ta mi'ka hannuta ta daura akan cinyoyinta a hankali cikin kwantar da murya tace
"haba ASMA'U kukan ya isa haka mana tun jiya kike abu daya sai kace wacce aka kashewa iyaye ya kamata kibar kukan nan haka kodan lafiyarki"
Wata kyakkyawan tsohuwa ta karbe zancen da cewa " ke da allah ya dubi maraicinki ya baki miji na bugawa a jarida. mijin da duk wacce ta sameshi ta gama more miji. kinsan yan mata nawa ne ke neman wannan damar amma allah bai basu ba ke ya baki, ba kuka ya kamata kiyi ba godema Allah ya kamata kiyi daya mallaka miki Muhammad aslam a matsayin mijin auren ki.
Koda yake bazan ma ce kiyi shiru ba. yi tayi kinga idan ASLAM ya zo ya sameki da ido jajur dole ya lallabo ya dawo wurina tinda dama nice uwargida ran gida nice ta karfen "
ta qarashe maganar cikin d'an zaulaya.
Matar datayi magana dazu ne ta sake cewa tana kallon mutane dakin"jama a ya kamata muyi haramar tafiya magariba Na gabatowa motocin da suka kawomu suna waje suna jiran mu Allah ya basu zaman lapiya" da amin wasu suka amsa a fili wasu a zuciya yayinda wasu ke fadin ba amin ba a zuciyarsu.
Wucewa duka yan kawo amaryan sukayi aka barta daga ita sai kawayenta kuma yan uwanta amira , zahra , da batool sai kuma kanwarta Khadijah.
*********************
Misalin karfe shidda da Rabi Na yammacin ranar asabar zaune yake a bakin gadon dakin hotel da ya kama yau kimanin kwana uku kenan.
sanye yake da singlet fari qal da wando 3quater, matashin sauryine Wanda a kalla zaikai shekara 30 da haihuwa.
Kallo daya zaka masa kasan dolenema yan mata su haukace akan shi domin ya gama haduwa ta ko ina. fatar jikinshi kawai idan ka kalla kasan Hutu da jin dadin sun gama zama a jikin shi komai Na jikin shi me kyau ne tun daga sumar kanshi mai dauke da baqin saisayayyen gashi mai taushin gaske, fusskarshi mai dauke da kyakkyawan bakin saje a zagaye dashi. ga kuma wani Dan madaidaicin gemu daya tsayar irin na samari yan kwalisa masu ji da gayu, zuwa yanayin tsarin halilltar jikinsa irin Na cikakkun maza masu kyawun sura, Muhammad aslam kenan ,aslam mutum ne Mara, son hayaniya shiyasa da wuya ka ganshi yana magana indai ba mai mahimmanci bane, akoda yaushe fuskarshi a kame take,
bai cika kyalkyata dariyaba saidai yayi murmushi .shima ba kowani lokaciba hakan yasa yan matan dake Neman kawo mishi wargi suke matugar shakkarsa. Yanada riqo da addini baya wasa da ibadah yana matuqar girmama iyayen shi hakan kuma ya samo asaline ganin yadda iyayen nashi ke girmama nasu iyayen suma, Abu daya ke bani mamaki ga rayuwarshi shine rashin son raini kwata kwata aslam baya son raini duk abinda zaiyi a rainashi ko cikin
abokaine bayaso balle kuma a gurin qannen shi, hakan yasa qannwnshi ke kwasan gwale-gwale a hannunshi baya wasa dash ko kadan tsakanin shi dasu girmamawane
Shere
And
Comment
Fisabillillah🙏🏻💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 5
Wayarsace dake gefensa ta fara ringing ko bai kalla ba yasan bazai wuce amir ba, miqa hannu yayi ya dauki wayar ya duba, kamar yadda yayi tsammani kuwa amir d'inne,
Kamar ko wani lokaci mayar da wayar yayi ya ajiye baiyi receiving ba, jota da biron da ke ajiye gefensa ya dauka,
sai da ya tsaya yayi Dan Jim kafin daga bisani yayi rubutun da bai wuce layi uku ba ya falle page din ya linke ya ajiye ,
Kallon agogo dake manne a dakin hotel din yayi ganin 6:40pm yasa ya mike ya shiga toilet domin ya dauro alwala,
Yana fitowa jallabiya ya dauka ya daura akan 'kananan kayan dake jikinsa. Paper da yayi rubutu da key ya dauka ya saka a aljihu ya fito d'akin d'auke da wayoyin shi a hannu ,
Kulle kofar dakin yayi ya fito a cikin hotel din ya nufi masallacin kusa da hotel din,
Daf da zai shiga masallacin wayarshi ta fara qarar alamar saqo ya shigo, Dan dakatawa yayi ya duba message din ganin saqon da aka turo ya saka shi dialing number da aka turo message din, picking akayi cike da girmamawa Wanda ya kira din ke fading
"yallabai gani nan Na karaso hotel din "
A daqile yace
"kasame ni a masallaci"
Ya kashe wayar ya shige cikin masallacin, saida aka idar da sallan magriba suka samu ganin juna, bayan sun gaisa hannu yasa a aljihu ya Ciro paper dayayi Dan note dazu ya miqa mishi tare da fadin. "ka kai ma waccen yarinyar"
Amsa yayi da hannu biyu amma ga dukkan alamu bai game wacce yarinya yake nufi ba , Dan sada kansa qasa kadan yayi alamar girmamawa sannan yace "yallabai wacce yarinya kake nufi"
Kallon shi aslam yayi ya dauke kai yace" yarinyar da suka kai gida Na dazu"
Murmushi ne ya kufce a fuskar bello yana Dan Sosa qeya yace
"yallabai amarya kake nufi"
Wani mugun kallo ya watsawa bello dayasa lokaci daya murmushin fuskarshi gimtsewa, Juyawa yayi zai wuce aiken da aka mai yana cewa "a huta lpy yallabai"
Saida yayi taku kamar biyar aslam ya kira sunan sa "bello" juyowa bello yayi ya dawo yadan risina yace "yallabai gani". Saida ya bushi iska yace "kada kowa yasan ina nan ciki harda daddy da amir, babu wani mahalukin dayasan inda nake sai kai kad'ai don haka take care" yana gama fadin haka ya duya ya shige cikin hotel din abinshi..
*********************
Bayan yan kai amarya sun wuce amira da zahra ne suka sakata a tsakiya akan tayi shiru ta daina kuka haka Allah ya qaddaro mata amma ina ko sauraronsu batayi sai kukanta takeyi bil hakki .
Khadijah CE itama ta matso gabanta ta tsuguna miqa hannu ta kama hannayenta ta riqe cikin muryan lallashi tace " yaya asmah ya kamata kibar kukan nan haka kada wani ciwo ya kamaki, idan fa wani Abu ya sameki Wanda kike kukan nan dalilin shi fa bashi da asara, muda muke sonki mukeda asara,mune zamu shiga wani hali idan wani Abu ya sameki pls yaya asmah ya isa haka"ta karashe maganar tana langwabar da kai idanunta cike da hawaye,
Dago kai tayi ta kallesu baba daya sai taga sun bata tausayi, share hawayen fuskarta tayi tare da qaqalo wani bushasshen murmushin da iyakacinsa fatar baki tayi musu,"Na gode yan uwana yanzu Ku tashi muyi sallah magriba yayi" ta fada tana zare hannunta cikin Na Khadijah, suma murmushin sukayi mata Khadijah Na fadin "yaya kokefa, don Allah karki qarayin kuka kinji " gyada mata kai kawai tayi,
Share
And
Comment
Fisabilillah🙏
Date: Sep 27, 2022
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Na sadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,
Allah kajiqan iyayen mu}
Page 6
A toilet din dake dakin gaba d'ayansu sukayi alwala banda batool dake kwance kan gado tana fashin sallah, hijjab da pray mat suka dauka a cikin sif kasance war an mata jerenta komai akwai a gidan hatta kayan sawanta suna cikin sit, zahra CE ta shiga wani app a wayarta ya nuna musu alqibla suka fara sallah,
Batool dake kwance taji kamar ana kwala sallama a kofar parlour saurarawa tayi still taji an sake yin sallamar, tashi tayi ta sauko parlour tana amsa sallamar,
Wani mutum ta gani me kimanin shekara arba'in , gaisawa sukayi cikin mutunta juna. Ya Dora da cewa"hajiya dama wani ne yazo yana waje wai mai gidan ne ya bashi saqo ya kawowa madam"
Sai lokacin batool ta fahimci waye wannan mutumin wato mai gadin ne,
"Kace yace yaya aslam ne ya aiko shi gurin asmah?"batool ta tambayeshi, "eh haka yace hajiya, yacema daga can babban gida yake"
"OK muje na ganshi" batool ta fada tana
nufar hanyar waje, bin bayanta mai gadi yayi suka fito compound din gidan,
Karasowa bello yayi ganin mai gadi da batool sun fito, batool tace"mallam bello dama kaine"
"Eh batool nine ya kike ya gujiba gujiban biki"
Batool tace "lpy qlau ya naka gujiba gujiban don nasan kaima kasha gujiba gujiban"Dan dariya yayi tare da cewa"wlh kuwa balool kaman kin Sani, Allah dai ya basu zaman lpy da zuri'a dayyibah "
"Amin thumma amin "batool ta amsa,
saka hannu bello yayi a aljihu ya d'auko farin takardar da aslam ya bashi ya miqawa batool"gashi kiba madam inji yallabai yace a kawo mata"amsa batool tayi tana jujjuya paper sannan tace"to shikenan mallam bello insha Allah yanzu inna shiga zan bata"
"Yawwa batool Na gode sai anjima"bello ya fad'a tare da juyawa ya wuce ,itama batool juyawa tayi ta shige parlon a ranta tana mamakin meye a cikin takar Dan nan da yaya aslam ya aiko dashi da bazai iya kira a waya ba
Koda ta dawo dakin kusan dukansu sun idar da sallah saidai suna zazzaune a gurin suna azkar d'insu, komawa tayi bakin gadon ta zauna tana jiran su idar ta miqa ma asmah saqon, zamanta kamar da minti biyar zahra ta miqe tana linke hijab,kallon batool tayi tace"wlh batool kedai anyi mara hankali"tana balla mata harara , itama batool hararan ta balla mata tare da cewa mai Na miki kuma uwar kankanba , tsaki zahra taja tare da cewa "kinzo kinhau gadon amarya ko kunya babu bayan kinsan sarai mummy ta hanamu hawa gadon mutane, kumama don tsabar rashin kunya gadon yaya aslam din kika hau, to wlh saina gayawa mummy" ,
Harara batool ta balla mata tace" to gulmammiya ba mummy zaki gayawa ba inkinga dama kije ki gayawa yaya aslam din da kanshi ya kasheni ko kuma kije ki gayawa alhaji baba qarewa"
Amira ce da itama idarwanta kenan tana like hijjab tayi gyaran murya uhummmmm duk juyowa sukayi suna kallon ta, itama su take kallo tace"
kudai kunji kunya wlh ko ina akaje sai kun sai kun raba hali sai kace wasu qananan yara"
Khadija ce ta kyalkyale da dariya tana cewa "
wlh twins din mummy kuna ban dariya"
kukan da sukaji asmah ta fashe da shine ya maida hankalinsu kanta, zaune take a inda ta yi sallah ta daga hannu sama tana kai kukanta gurin mahaliccinta, sosai take addu'a akan aurenta da Neman mafita mafi alkhairi, dukkan su da amin suke amsawa har ta gama ta shafa suma suka shafa tare da ita,
batool ce ta matsa kusa da ita tare da miqa mata paper da bello ya kawo tana fadin "amaryan yayanmu wai gashi inji angon naki ya aiko mallam bello direba dazu kina sallah wai ya kawowa shibarsa" ta fada cikin sigar zaulaya,
Dago kanta tayi ta Dan qurawa pepan dake hannnun batool ido kafin ta mika hannu ta karba, bud'e pepan tayi ta qurawa rubutun da baifi layi uku ba ido,
Karantawa takeyi tana qara maimaita karanta abinda ke cikin pepan a zuciyarta. ganin dai tabbas abinda ta gani arubuce a cikin paper tabbas haka yake ba gizo idanunta ke mata ba,ya sata sakin wani qayataccen murmushin Wanda yasa yan biyu mummy da amira da khadija kallon kallo a tsakanin su,
Zahra ce datafi kusa da ita ta miqa hannu ta karbi papern a hannunta warwarewa tayi ta fara karan tawa da qarfi yanda sauran zasu jita kamar haka
Share
And
Comment
Fisabilillah🙏🏻
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Na sadaukar da wannnan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,
Allah ka jiqan iyayen mu}
Page 7&8
Ni muhammad aslam na saki matata asma'u saki daya saboda bana sonta bana kaunarta Na tsaneta,,(😱😱😱).
Batool ne ta fizge pepan dake hannun zahra tana qara karantawa a zuciyarta don ita bata yarda abinda zahra ta karanta musu dai-dai bane, amira kuwa miqewa tsaye tayi hannunta dafe da girjinta tana zazzaro ido waje kamar wacce aka koda ma marin bazata sai maimaita innalillahi wa innailaihi raji'un takeyi a baiyane,
Khadijah kuwa rarrafawa tayi ta qarasa gaban asmah tana jijjigata tama rasa mai zatace bakinta sai motsi yakeyi amma maganar taqi fitowa,
Asmah ce ta bige hannun Khadijah daketa faman jijjigata ta miqe tsaye da qarfinta fuskarta dauke da kayatatcen murmushi kamar ba ita bace keta kuka mintuna kadan da suka wuce,
Gyara zaman hijjab din jikinta tayi tana kallonsu tace "dama Na Sani Allah bazai taba barina haka ba, zai kawo min dauki arayuwata, domin dashi Na dogara kuma duk Wanda ya dogara da Allah to Allah ya Isar masa a komai" daga hannu tayi sama fuskarta dauke da murmushi tace "alhamdulillahi,, alhamdulillahi ,,alhamdulillahi ,, Allah Na gode maka"
Amsar pepan tayi a hannun batool ,ta dauki wayarta dake ajiye kan mirror, sannan tace musu "kumuje gida ko" dukkansu sanqarewa sukayi suna kallon